Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Pankshin/Kanke/Kanam a Jihar Filato, Yusuf Gadgi, ya zargi wasu ‘yan adawa da amfani da matsalar rashin tsaro domin cimma muradun siyasa gabanin zaɓen 2027.
Da yake magana a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels a ranar Talata, Gadgi ya ce rashin tsaro babbar matsala ce da ta shafi ƙasa baki ɗaya, amma bai kamata a mayar da ita siyasa ba.
Ya ce wasu daga cikin ‘yan adawa sun fi mayar da hankali wajen zargin gwamnatin tarayya da gazawa maimakon gabatar da hanyoyin magance matsalar.
Haka kuma, ya bayyana mamakinsa yadda hare-hare ke ƙaruwa yayin da ake shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.
Ɗan majalisar ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su kasance masu haɗa kai da kishin ƙasa, tare da ɗora alhakin kare rayuka da dukiyoyi a kan gwamnati ba tare da mayar da matsalar rashin tsaro siyasa ba.
Kalaman nasa na zuwa ne yayin da ake ci gaba da nuna damuwa kan yawaitar hare-hare a sassa daban-daban na ƙasar da kuma sukar yadda gwamnati ke tunkarar matsalar rashin tsaro.













