Gwamnatin Iran ta sanar da cewa za ta rufe babban birnin ƙasar, Tehran, a ranar Talata 7 ga watan Yuli domin gudanar da jana’izar Ayatollah Ali Khamenei.
Mai magana da yawun gwamnati, Fatemeh Mohajerani, ta ce an ɗauki wannan mataki ne domin sauƙaƙa zirga-zirgar dubban mutane da ake sa ran za su halarci jana’izar, tare da ba su damar komawa gidajensu cikin sauƙi.
Haka kuma, gwamnatin ta ayyana ranar Alhamis a matsayin ranar zaman makoki a faɗin ƙasar.
Ana sa ran za a binne Ayatollah Khamenei a birnin Mashhad a ranar Alhamis.
Za a gudanar da bukukuwan jana’izarsa a biranen Tehran, Qom da Mashhad daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli.
Za a kuma gudanar da bukukuwan tunawa da shi a biranen Bagadaza, Kazimain, Karbala da Najaf na ƙasar Iraki.
Ayatollah Ali Khamenei ya rasu ne bayan hare-haren sama da Amurka da Isra’ila suka kai a Iran, inda aka kai hari a gidansa.













