An kashe Hakimin Gundumar Gwande da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos a Jihar Filato bayan wasu ‘yan bindiga sun kai masa hari a hanyar dawowarsa daga taro.
Marigayin, Saf Samuel Alaket, an kai masa farmaki ne a daren ranar Talata a kan hanyar Sha zuwa Daffo.
Majiyoyi sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:30 na dare, lokacin da yake dawowa gida bayan halartar taron sarakunan gargajiya a Bokkos.
Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun tare motarsa kusa da iyakar Sha da ƙauyen Daffo, sannan suka buɗe masa wuta.
An ce ya samu munanan raunuka, kuma an garzaya da shi wani asibiti domin ba shi agajin gaggawa, amma daga baya ya rasu.
Mazauna yankin sun bayyana mutuwarsa a matsayin babban rashi ga al’ummar Gwande da dukkanin yankin Bokkos.
Wani mazaunin yankin, Mists Aten Pukat, ya ce mutuwar ta jefa al’umma cikin jimami.
Shugaban matasan yankin, Christopher Luka, ya ce harin ya jawo tashin hankali, amma daga baya an samu daidaituwar al’amura a yankin.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ‘yansanda a Jihar Filato ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.















Discussion about this post