Wasu ’yan bindiga dauke da makamai sun kai hari ranar Asabar a kauyen Ekerin da ke karamar hukumar Ekiti a jihar Kwara, inda suka kashe masu ibada uku tare da yin garkuwa da wasu 15 daga wani coci.
Maharan sun kai harin ne da misalin karfe 10:30 na dare a wurin da masu ibadar ke gudanar da ibada ta tsakar dare.
LEADERSHIP ta rawaito cewa ’yan bindigar sun rika harbe-harbe sama domin tsoratar da jama’a kafin su kutsa kai zuwa Ori-Oke Ajaiye inda masu ibadar ke gudanar da ibadar ta tsakar dare.
Rundunar ’yansandan jihar, a cikin wata sanarwa da kakakinta Adetoun Ejire-Adeyemi ta sanya wa hannu ranar Lahadi, ta tabbatar da kashe masu ibada uku tare da sace wasu 15 da ’yan bindigar suka yi.















Discussion about this post