’Yan bindiga dauke da makamai sun kashe mutane 21 a kauyen Bunkasau da ke karkashin gundumar Zarummai a karamar hukumar Bukkuyum ta jihar Zamfara.
Maharan, wadanda aka kiyasta sun haura 80, sun iso ne a kan babura inda suka bude wuta kan mazauna yankin, tare da yin garkuwa da mutane da dama, galibinsu mata, sannan suka kwashe dabbobi.
- Buƙatar Taimaka Wa Al’umma Ba Sai Sun Yi Roƙo Ba
- INEC Ta Gargaɗi Jam’iyyu Kan Gudanar Da Babban Taro Ba Tare Da Sanin Ta Ba
Wani mazaunin kauyen da ya nemi a sakaya sunansa, a wata hira da aka yi da shi, ya ce harin ya faru ne da daren Juma’a.
A cewarsa, har yanzu mazauna yankin na ci gaba da neman mutanen da suka bace.
Ya kara da cewa ana ci gaba da shirye-shiryen jana’izar wadanda suka rasu.
Haka kuma ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jihar Zamfara da su kawo dauki ta hanyar tura jami’an tsaro zuwa yankin domin dawo da zaman lafiya.
Da aka tuntubi kakakin rundunar ’yansanda, DSP Yazid Abubakar, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, har yanzu ba a tantance adadin wadanda suka mutu ba.
A cewarsa, rundunar ta tura isassun jami’an tsaro zuwa yankin, tare da fatan an dawo da zaman lafiya.















Discussion about this post