ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Gargaɗi Jam’iyyu Kan Gudanar Da Babban Taro Ba Tare Da Sanin Ta Ba

by Yusuf Shuaibu and Abubakar Sulaiman
2 months ago
inec

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), Joash Amupitan, ya gargaɗi jam’iyyar ADC kan ci gaba da shirya babban taronta na ƙasa ba tare da sa idon hukumar ba.

Amupitan ya bayar da gargaɗi ne yayin wata hira a gidan talabijin na Arise a ranar Juma’a, bayan jam’iyyar ta dage kan ci gaba da babban taronta na ƙasa duk da ƙin amincewar INEC na shugabancin da ke da alaƙa da Sanata Daɓid Mark da Rauf Aregbesola.

Ya jaddada cewa matakin INEC ta dogara ne kan la’akari da shari’a, musamman umarnin kotu da ake da shi.

ADVERTISEMENT

“Saboda haka, idan suna ci gaba da shirin gudanar da babban taron jam’iyyar na ƙasa, ya rage garesu, domin hakan ya saba wa shari’a. INEC ba kawai ta yanke ɗauki matakin ba ne haka nan. Ba mu tashi kawai haka nan mun yanke wannan hukunci ba. Akwai wani abu da ya kai ga haka. Akwai wata doka ta kotu,” in ji shi.

A cewarsa, kotu ta umarci ɓangarorin ka da su ɗauki matakan da za su iya kawo cikas ga shari’o’in da ke gudana.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Ka da ka yi komai. Ka da ka ɗauki wani mataki wanda zai sa kowace shari’a a gaban kotu ta zama babu amfani,” in ji Amupitan.

Ya bayyana cewa batun gudanar da babban taron jam’iyyar na ƙasa ya kasance wani ɓangare na tsarin shari’a da ake jira.

“Don haka, idan har yanzu suna tambaya cewa ka da a yi kowanne taro na jam’iyya, ka da a yi kowanne taro na jam’iyyar, hakan wata sauƙi ce da ake iƙirarin samu. Kuma sun shigar da wani buƙƙata don wannan dalili, har yanzu ba a yanke hukunci kan wancan buƙata ba,” ya ƙara da cewa.

Shugaban INEC ya yi gargaɗin cewa yin watsi da umarnin kotu na iya haifar da mummunan sakamako, yana kawo naƙasu kan zaɓuka da suka gabata.

“Bari in gaya muku abin da ya faru a Zamfara. Ya faru a baya. Ba ma son gudanar da zaɓe ba tare da wannan gargaɗi ba, kuma a ƙarshen rana, bayan kun yi nasara, kotu za ta sake zuwa ta ayyana zaɓen a matsayin mara inganci. Kuma ma’anar ita ce mutumin da ya fi yawan ƙuri’u na biyu za a ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

“Abun ya faru a Jihar Filato a zaɓen da ya gudana, sakamakon rashin bin umarnin kotu wanda ke da illar gaske,” in ji Amupitan.

Yayin da yake jaddada cewa ADC na da ƴancin yin abin da ta ga dama, ya jaddada cewa INEC ba za ta maimaita kura-kuran da aka yi a baya ba.

“Suna da ƴanci su yi duk abin da suke so su yi, amma INEC ba za ta maimata kuskuren da ta yi a baya ba,” in ji shi.

 

Inec
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Inec
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

NPA Ta Ƙuduri Aniyar Inganta Tashar Jiragen Ruwa Ta Apapa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.