Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), Joash Amupitan, ya gargaɗi jam’iyyar ADC kan ci gaba da shirya babban taronta na ƙasa ba tare da sa idon hukumar ba.
Amupitan ya bayar da gargaɗi ne yayin wata hira a gidan talabijin na Arise a ranar Juma’a, bayan jam’iyyar ta dage kan ci gaba da babban taronta na ƙasa duk da ƙin amincewar INEC na shugabancin da ke da alaƙa da Sanata Daɓid Mark da Rauf Aregbesola.
Ya jaddada cewa matakin INEC ta dogara ne kan la’akari da shari’a, musamman umarnin kotu da ake da shi.
“Saboda haka, idan suna ci gaba da shirin gudanar da babban taron jam’iyyar na ƙasa, ya rage garesu, domin hakan ya saba wa shari’a. INEC ba kawai ta yanke ɗauki matakin ba ne haka nan. Ba mu tashi kawai haka nan mun yanke wannan hukunci ba. Akwai wani abu da ya kai ga haka. Akwai wata doka ta kotu,” in ji shi.
A cewarsa, kotu ta umarci ɓangarorin ka da su ɗauki matakan da za su iya kawo cikas ga shari’o’in da ke gudana.
“Ka da ka yi komai. Ka da ka ɗauki wani mataki wanda zai sa kowace shari’a a gaban kotu ta zama babu amfani,” in ji Amupitan.
Ya bayyana cewa batun gudanar da babban taron jam’iyyar na ƙasa ya kasance wani ɓangare na tsarin shari’a da ake jira.
“Don haka, idan har yanzu suna tambaya cewa ka da a yi kowanne taro na jam’iyya, ka da a yi kowanne taro na jam’iyyar, hakan wata sauƙi ce da ake iƙirarin samu. Kuma sun shigar da wani buƙƙata don wannan dalili, har yanzu ba a yanke hukunci kan wancan buƙata ba,” ya ƙara da cewa.
Shugaban INEC ya yi gargaɗin cewa yin watsi da umarnin kotu na iya haifar da mummunan sakamako, yana kawo naƙasu kan zaɓuka da suka gabata.
“Bari in gaya muku abin da ya faru a Zamfara. Ya faru a baya. Ba ma son gudanar da zaɓe ba tare da wannan gargaɗi ba, kuma a ƙarshen rana, bayan kun yi nasara, kotu za ta sake zuwa ta ayyana zaɓen a matsayin mara inganci. Kuma ma’anar ita ce mutumin da ya fi yawan ƙuri’u na biyu za a ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen.
“Abun ya faru a Jihar Filato a zaɓen da ya gudana, sakamakon rashin bin umarnin kotu wanda ke da illar gaske,” in ji Amupitan.
Yayin da yake jaddada cewa ADC na da ƴancin yin abin da ta ga dama, ya jaddada cewa INEC ba za ta maimaita kura-kuran da aka yi a baya ba.
“Suna da ƴanci su yi duk abin da suke so su yi, amma INEC ba za ta maimata kuskuren da ta yi a baya ba,” in ji shi.















Discussion about this post