Shafi ne da ya saba zaƙulo muku fitattun jaruman finafinan hausa manya da ƙanana, daga cikin masana’antar shirya finafinan hausa ta Kannywood. A yau shafin ya yi cozali da wata fitacciyar jarumar wacce ta shahara ta ga jiya ta ga yau a cikin masana’antar shirya finafinan hausa ta Kannywood wato, FATI MUHAMMAD Inda ta warwarewa masu karatu zare da abawa game da cece-kucen da wasu ke yi na jita-jitan da aka yaɗa a kanta. Har ma da wasu bayanan da suka shafi rayuwarta.
Ga dai tattaunawar tare da wakiliyar Jaridar LEADERSHIP HAUSA RABI’AT SIDI BALA Kamar haka:
Fati Muhammad ba kya buƙatar doguwar gabatarwa, sai dai kasancewar akwai shekaru da yawa da ki ka shafe a cikin masana’antar Kannywood, masu karatu za su so su ji shin wace ce Fati Muhammad?
Da farko dai sunana Fati Muhammad, Fati Muhammad dai bafulatana ce, kuma ni haifaffiyar jihar Kano ce. An haife ni a garin Kano a unguwar Tukuntawa a nan nayi ‘Primary School’ ɗina da sauran abubuwana har na shiga fim. Bayan fim sai aka yi.min aure na zo na tafi zuwa ƙasar England, wannan shi ne a taƙaice.
- Ban Fuskanci Matsala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Asiya Muhammad
- Ban Taba Da-Na-Sanin Shiga Harkar Fim Ba —Rukayya
Wasu na raɗe-raɗin cewa, kin ce kin yi da-kin-sanin shiga harkar fim, shin mene ne gaskiyar maganar?
To, ni dai na yi hira da Ali Jita, kuma hirar ta fita, a zahirin gaskiya ni ma haka nake gani. Kamar yanzu a ay a da ake cewa nayi da-na-sanin shiga harkar fim, gaskiya ni Fati Muhammad ban taɓa makamanciyar irin wannan maganar ba tunda nake. Ai babu ma ta yadda za a ay a ce nayi da-na-sanin shiga fim a rayuwata, ai ay a min riga, ya yi min wando, ya min dukkan wata sutura a rayuwa. Duk wani mataki da na kai, da matsayin da nake akai har gobe da kuma dukkan alkhairan da nake samu a gurin al’ummar Annabi to, darajar fim ne. Saboda haka babu yadda za a ay a ce nayi da-na-sanin shiga fim ban taɓa wannan ay a ba tunda nake a rayuwata ta duniya. A kowane kafar sada zumunta ko kafafen yaɗa labarai na jaridu, ban taɓa irin wannan maganar ba gaskiya. Na ay aa ina alfahari da fim, duk da ay a na daina yin fim amma ay a raina fim ba, domin a rayuwata ta duniya ay a yi min dukkan abin da zan yi. Yau a matakin da nake ciki nake shiga inda matsayina bai kai in kai ba darajar fim ne, nake samun kyaututtuka da nasarori da ci gaba duk darajar fim ne. Har na kai matsayin da ba na tunani na ƙasashen ƙetare gida da waje, ma’ana ace na tattara ina fita ƙasashen waje da kuma Africa da kuma gida nan Najeriya to, duk darajar fim ne.
Kasancewar kin ga jiya kin ga yau a cikin masana’antar Kannywood, ya za ki bambantawa masu karatu yadda masana’antar Kannywood take a lokutan baya da kuma yanzu?
Ayan zan kuma daina ay aa akwai bambance-bambance sosai a masana’antar Kannywood baya da yanzu, ci gaba a yanzu an samu ta ɓangaren kayan aiki da sauransu, yadda hotonmu yake a baya da kuma yanzu akwai bambanci. Sannan ta ɓangaren jarumai mu a baya ba mu da yawa bamu wuce mutum goma zan ce ba ko sha, saɓanin na yanzu matan suna da yawa, kuma bahaushe na cewa; “Idan Dambu ya yi yawa- ay a jin mai”. Bambancinmu da ay a ne, yawancinku mu da yawa mun zo ne sana’a da neman suna, ban ce su ma ay a suka zo nema ba amma ‘majority’ wasu ba sana’a suka zo yi yanzu ba. Akwai waɗanda sun zo neman suna ne da sana’a, amma ay a da yawa ƙalilan ne, wasu za a ga sun zo kawai domin neman suna su yi amfani da wannan sunan domin su cimma burukansu. Mu kuma sunan muka nema kuma Allah ay a mu, kuma har gobe muna cin gajiyar wannan sunan da muka samu. Gaskiya akwai bambanci ko daga wurin ‘acting’ ɗinmu da su akwai bambanci da yadda ake ɗaukar abun. Dan wasu na cewa sun fi son su kalli fim ɗin ‘da’ akan na yanzu, ba wai dan nayi fim a baya yanzu ba na yi ba, sai dan saboda za su ce fim ɗin da’ ya fi ma’ana da sauransu.
Ko akwai wani gyara ko cigaba da ki ke ganin ya kamata shuwagabannin masana’antar Kannywood su ƙara zage dantse wajen kawo ci gaban masana’antar?
Shuwagabannin masana’antar Kannywood na san bakin gwargwado wanda Allah ya ɗorawa alhakin su kawo gyaran, wasu daga ciki suna bakin gwargwadonsu. Kamar yanzu misali abin da yake faruwa, idan mutum ɗaya yayi laifi ko kuma.na ce ‘ya mace tayi wani abu wanda bai dace ba a masana’ar, tunda matan mun fi kura-kurai akan maza. Maimakon ace yau an bayar da ‘punishment’ ko kuma an dakatar da wance, sai ka ji wasu ɓangaren ko furodusas sun ce “dan me?, ai ay a wanda ya isa ay a ya dakatar da wancen zan saka ta a aikina”, kin ga yadda za a yi gyara ya tafi a haka, domin sai an haɗa ƙarfi da ƙarfe sannan za a kawo gyaran. Kuma masana’antar nan a nan ne ake ci ake sha, nan ake ci da iyaye, wasu nan suke ci da iyalansu, da ƴan’uwansu da komai to, me ya kamata? Sai a ce an haɗa ƙarfi da ƙarfe an kawo gyara, tunda akwai gurɓatattu a ciki, wanda suke ɓata sunan harkar, suke gurɓata harkar wanda ay a wasu bane ‘Astagfrillah’ ba wai nayi alfahari ba. Idan yarinya tayi abu mara kyau sai ta ce ita ‘yar fim ce, idan aka tashi ba za a duba wane fim tayi ba, a’ina aka santa? Sai a yi kuɗin goro sai a ga abubuwa mara daɗi ya zo.
Mutane da dama za su so su ji, me ya ja hankalinki har ki ka rikiɗa daga harkar fim zuwa siyasa?
Mu ƴan Hausa fim ƴan Kannywood mu ne mutane suke ganin dan me ya sa dan muna yin fim ba za mu zo mu shiga harkar siyasa ba, ko a America idan ka je akwai.manyan ‘celebrities’ ƴan America da suke tsayawa ma ay a, su fito neman gwamna, wanni senata, Wani can majalisa, ko a Indiya da yawansu suna fitowa suna yi ina ganin ba wani abu bane, mune dai nan idan ka fito sai a ga abun ya bambanta to, ni kawai ra’ayina ne. Na ga ah! Tunda ina da ‘stardom’ a duniya, me zai hana ni ma na shiga siyasa a dama da ni, ay aan iya bayar da wata gudunmawa a ƙasa ta Najeriya.
Ko akwai wani ƙalubale da ki ka taɓa fuskanta game da siyarsar da ki ka shiga a yanzu?
Ba za a rasa ƙalubale ba tunda gaskiya ni ay aa siyasa ne tun a jam’iyyar PDP, daga baya kuma sakamakon na ɗan fuskanci ƙalubale wurin ƴan adawa da kuma al’ummar Annabi wanda suke ganin ya za a ay a tsallako ay a zan shiga harkar siyasa, duk da ba ay a na ay aa ina tallata ɗan takarata ne, ina amfani da sunan da Allah ay a ni ina tallata wanda nake so. Na fuskanci ƙalubale da yawa sosai, amma ni wannan ay a damuna. Duk abin da za ka yi a rayuwa dole za ka fuskanci ƙalubale kala-kala da tsangwama, kuma idan ka yi haƙuri zai zo ya wuce.
Za mu ci gaba a makon mai zuwa inshaAllah















Discussion about this post