Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.
A yau zan yi jan hankali ne ga ɗaukacin musulmi gaba ɗaya a duk inda suke, ba iya maza ba har ma da matan. Muna da wata ɗabi’a, da ta shiga zuciyarmu yanzu, za ka ga idan kana tare da mutum ko da kun fi shekara goma sha ko ashirin, wani ma tare kuka taso, za ka ga wasu Allah ya rufa musu asiri a ciki.
Kuma akwai wanda da kyar ma yake iya siyan abinci ya kai wa iyalinsa, wai idan bai roƙa ba, ba za a iya taimaka masa ba, kuma ana ji ana kallo.
- Sin Ta Samun Gaggarumin Ci Gaban Ayyukan Taimakon Masu Bukata Ta Musamman
- Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo
Haba ƴan’uwa musulmi, “Almuslumu akul muslum” Annabi ne ya faɗa, duk inda musulmi yake ɗan’uwan musulmi ne, ballantana wanda aka taso.
Wasu ma za a ga jini ɗaya ne, amma mutum yana cikin wani yanayi kai ka san ka ninninka shi a samu, ƙila ba ya iya siyan abincin yau da gobe a gidansa, kullum sai ya sayi wanda za a dafa, kai kuma akwai na wata ɗaya ko biyu a gidanka, amma wai sai ya roƙe ka za ka taimake shi, idan bai roƙe ka ba, ba za ka iya taimakonshi ba.
Wannan ba daidai ba ne ba, wannan ba tausayi bane ba, ba halayya ce ta musulmi ba, ba ɗabi’a ce irinta sahabbai ba, ba halayya ce ta Annabawa ba.
Akwai tausayawa, akwai zumunci, ka taimakawa ɗan’uwanka musulmi ba sai ya nemi taimakonka ba, kai ka san ya kamata ka taimaki wane. Sai ka ga mutum ya mutu, sai akai buhun shinkafa, wai ana taimakawa iyalansa, wannan ƙarya ne, mugunta ce, ba daidai bane ba. Wani ya yi fafutuka tsawon shekara ashirin ko talatin yana ta neman ko da rabin kwata ne ya sayawa iyalansa, ba za a iya taimaka masa ba, kuma Allah ya taimaka masa.
A ciki ma za ka ga akwai wanda zai iya saya masa gidan, ya bashi mota, ya bashi jari, amma ba za a yi ba, wai sai ya mutu sai a je a ɗan sayarwa iyalansa gida.
Kai ka ji wani rashin tunani, ka taimakawa mutum tun da rayuwarsa da lafiyarsa, kai ko bashi ne mutum kake binsa, ya kamata tunda ransa da lafiyarsa ka bashi ya je ya biya.
Waye ba a bi bashi, idan mutum ba shi da hali kai ka sani, kana tare da shi ka taimaka masa ya ji daɗi. Ƴan’uwa idan muna so mu ga daidai, mu ƙare rayuwarmu lafiya sai mun taimaki ƴan’uwanmu. Wallahi ɗabi’un da muke bi, muke ɗauka ba daidai bane ba.
Mu taimakawa mutum ba sai ya kasa ba, ya kwanta ya kasa tashi, ko yunwa da talauci sun kashe shi, sannan zamu je mu kai wa iyalansa buhun shinkafa, haba wannan ba ɗabi’ar kirki ba ce ba.
Mu taimakawa mutane suna neman taimako, wani ko shekara ɗari zai yi ba zai tambaya ba, idan ka san kana tare da mutum yana neman taimako ka taimake shi ba sai ya tsuguna yana neman taimakon ka ba, ba sai ya kira ka a waya ya zubar da mutuncinsa ba.















Discussion about this post