Wasu ’yan bindiga dauke da makamai sun mamaye al’ummar Yashikira da ke karamar hukumar Baruten ta jihar Kwara a daren Lahadi, inda suka yi garkuwa da mutane 10, sannan kuma suka farmaki fadar Sarkin Yashikira da ofishin ’yansanda da ke kusa.
Majiyoyi sun bayyana cewa maharan sun kai harin ne acikin duhun dare, inda suka fara kai wa fadar Sarkin Yashikira da cibiyoyin ’yansanda hari kafin jami’an tsaro su kore su.
An kuma rahoto cewa, gaggawar martanin jami’an tsaron ta taimaka wajen hana maharan kai wa wasu wuraren da suka yi nufi hari.
Wani babban jami’in tsaro da ya tabbatar da faruwar lamarin ga LEADERSHIP ya ce haɗin gwiwar tawagar sojoji da ’yansanda ta fara gudanar da aikin ceto domin kuɓutar da mutanen da aka sace.















Discussion about this post