Tsohon sanatan da ya wakilci Kano ta Kudu a Majalisar Dattawa ta 9, Kabiru Ibrahim Gaya, ya rasa tikitin komawa majalisar karkashin jam’iyyar NDC.
Gaya, wanda ya koma jam’iyyar NDC kwanan nan bayan ficewarsa daga jam’iyyun APC da ADC, ya biyo bayan cimma yunkurinsa na komawa Majalisar Dattawar ne.
Sai dai ya sha kaye wajen samun tikitin jam’iyyar a hannun tsohon shugaban kungiyar masu motocin haya ta kasa, (NARTO), Alkasim Ibrahim Batayya.
Mataimakin mai magana da yawun Kwankwasiyya, Mansur Kurugu, ya tabbatar da cewa Batayya ya samu tikitin ne ta hanyar maslaha da aka gudanar a gidan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da ke Miller Road a Kano ranar Lahadi.
Kurugu ya kara da cewa, “Kabiru Gaya ya riga ya amince da hukuncin tare da yin alkawarin bayar da cikakken goyon baya domin Batayya ya lashe kujerar.”
Ya ce zaman maslahar zai ci gaba ranar Litinin har sai an tantance dukkan kujerun ba tare da sai an gudanar da zaben fidda gwani ba.















Discussion about this post