Wasu da ake zargin ‘yan daba ne sun farmaki mutane a ranar Talata a shahararriyar kasuwar wayoyin hannu ta ‘Farm Center’ a Kano, lamarin da ya haddasa firgici tsakanin ‘yan kasuwa da masu saye.
Wata majiya daga kasuwar ta shaida wa ‘THR News’ cewa maharan, waɗanda ake zargin sun fito daga wani taron siyasa da ɗan takarar Sanatan Kano ta Tsakiya, A.A. Zaura, ya shirya, sun farmaki sashen Yoyo Plaza ne dake kasuwar.
A cewar majiyar, ‘yan daban sun kai wa ‘yan kasuwa hari tare da tarwatsa harkokin kasuwanci da ake gudanarwa, wanda ya haddasa firgici a yankin.
An kuma rawaito cewa, sun ƙwace wayoyin hannu na mutanen da ke kan harkokinsu a kusa da kasuwar.
Daga bisani jami’an tsaro, ciki har da ‘yansanda, sun isa wurin inda suka samu nasarar tarwatsa maharan.Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a tabbatar da samun asarar rayuka ko jikkata ba sakamakon harin.















Discussion about this post