ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

by Abubakar Sulaiman
5 hours ago

Rundunar ‘yansandan jihar Katsina ta yi nasarar kama wasu mutane biyar da ake zargi da haɗin baki da sata da kuma siyar da wayoyin wutar lantarki na gwamnati a yankin Bugaje da ke Ƙaramar Hukumar Jibia. Kakakin rundunar, DSP Abubakar Sadiq-Aliyu, ne ya tabbatar da hakan, inda ya bayyana cewa an kama mutanen ne bayan samun sahihan bayanan sirri da jami’ansu suka bibiya.

Binciken farko ya nuna cewa, asalin wayoyin lantarkin sun faɗo ƙasa ne a garin Bugaje sakamakon wata iska mai ƙarfi da aka yi a yankin, inda shugabannin al’ummar yankin suka kwashe su suka ajiye su domin tsaro. Sai dai waɗanda ake zargin suka haɗa baki suka raba sassan wayoyin da aka ajiye, sannan suka yi awon gaba da su domin siyarwa ba tare da izini ba.

Mutane ukun farko da aka kama da laifin satar sun haɗa da Hassan Ibrahim mai (shekara 30), da Lawal Ibrahim (shekara 31), da Abubakar Sani (shekara 31). Haka kuma, binciken ya bankaɗo Umar Isa (shekara 35) wanda shi ne ya kwashe kayan sannan ya siyar da su ga wani shahararren mai sayen kayan sata a yankin mai suna Ibrahim Rabiu (shekara 27).

ADVERTISEMENT

Yayin da jami’an tsaro suke yi musu tambayoyi, waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu inda suka bayyana cewa sun siyar da wayoyin lantarkin ne a kan kuɗi naira dubu ɗari uku (N300,000). Bayan haka, jami’an tsaron sun yi nasarar ƙwato wasu ƙofofin ƙarfe guda 10 da aka sato daga rukunin gidaje na Barawa Estate, tare da wasu kayayyakin lantarki da tsofaffin ƙarafa da aka adana.

A halin yanzu, rundunar tana ci gaba da farautar wasu mutane bakwai da waɗanda aka kaman suka ambata a matsayin abokan burmimminsu waɗanda suka gudu. Kwamishinan ‘yansandan jihar, Aliyu Umar-Fage, ya yi gargaɗi mai tsanani ga masu lalata kayayyakin gwamnati, inda ya jaddada cewa za a miƙa mutanen gaban kotu da zarar an kammala bincike.

LABARAI MASU NASABA

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
  • Abubakar Sulaiman
    Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni
  • Abubakar Sulaiman
    Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

MASU ALAKA

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi
Manyan Labarai

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni
Manyan Labarai

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.