Rundunar ‘yansandan jihar Katsina ta yi nasarar kama wasu mutane biyar da ake zargi da haɗin baki da sata da kuma siyar da wayoyin wutar lantarki na gwamnati a yankin Bugaje da ke Ƙaramar Hukumar Jibia. Kakakin rundunar, DSP Abubakar Sadiq-Aliyu, ne ya tabbatar da hakan, inda ya bayyana cewa an kama mutanen ne bayan samun sahihan bayanan sirri da jami’ansu suka bibiya.
Binciken farko ya nuna cewa, asalin wayoyin lantarkin sun faɗo ƙasa ne a garin Bugaje sakamakon wata iska mai ƙarfi da aka yi a yankin, inda shugabannin al’ummar yankin suka kwashe su suka ajiye su domin tsaro. Sai dai waɗanda ake zargin suka haɗa baki suka raba sassan wayoyin da aka ajiye, sannan suka yi awon gaba da su domin siyarwa ba tare da izini ba.
Mutane ukun farko da aka kama da laifin satar sun haɗa da Hassan Ibrahim mai (shekara 30), da Lawal Ibrahim (shekara 31), da Abubakar Sani (shekara 31). Haka kuma, binciken ya bankaɗo Umar Isa (shekara 35) wanda shi ne ya kwashe kayan sannan ya siyar da su ga wani shahararren mai sayen kayan sata a yankin mai suna Ibrahim Rabiu (shekara 27).
Yayin da jami’an tsaro suke yi musu tambayoyi, waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu inda suka bayyana cewa sun siyar da wayoyin lantarkin ne a kan kuɗi naira dubu ɗari uku (N300,000). Bayan haka, jami’an tsaron sun yi nasarar ƙwato wasu ƙofofin ƙarfe guda 10 da aka sato daga rukunin gidaje na Barawa Estate, tare da wasu kayayyakin lantarki da tsofaffin ƙarafa da aka adana.
A halin yanzu, rundunar tana ci gaba da farautar wasu mutane bakwai da waɗanda aka kaman suka ambata a matsayin abokan burmimminsu waɗanda suka gudu. Kwamishinan ‘yansandan jihar, Aliyu Umar-Fage, ya yi gargaɗi mai tsanani ga masu lalata kayayyakin gwamnati, inda ya jaddada cewa za a miƙa mutanen gaban kotu da zarar an kammala bincike.















Discussion about this post