Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya, FIFA ta tabbatar da cewa za ta biya alƙalin wasa ɗan ƙasar Somalia, Omar Artan, cikakken kuɗaɗensa na gasar cin kofin duniya ta shekarar 2026.
Wannan mataki ya biyo bayan hana shi shiga ƙasar Amurka da jami’an tsaron ƙasar suka yi, wanda hakan ya sa ba zai iya yin alƙalanci a gasar ba. Jami’an tsaron iyakokin Amurka sun tsare Omar Artan na tsawon sa’o’i 11 a filin jirgin sama na Miami, inda suka soke bizar tasa saboda zargin yana da alaƙa da ƙungiyar ta’addanci ta AlShabaab,
zargin da alƙalin wasan ya musanta.
Amma tun da yake dukkan alƙalan wasa dole ne su zauna a sansanin horarwa da ke Florida, rashin bizar Amurka ya hana shi damar yin alƙalanci ko da a ƙasashen Canada da Meɗico ne.
Sai dai duk da wannan komabaya, Artan ya koma gida Mogadishu inda aka tarbe shi kamar gwani. Sannan kuma, hukumar ƙwallon ƙafa ta Turai wato UEFA ta karrama shi ta hanyar ba shi damar jagorantar babban wasan kofin “UEFA Super Cup” tsakanin PSG da Aston Ɓilla a watan Agusta mai zuwa.















Discussion about this post