ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

by Sulaiman and Shehu Yahaya
3 weeks ago
Matasa

Matasa maza da Mata 1,200 ne suka amfana da horon sana’o’i da tallafin jari a ƙaramar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna karkashin shirin “Renewed Hope Empowerment Initiative” Na Shugaba Bola Tinubu da Gwamna Uba Sani.

Shirin, wanda aka gudanar domin inganta tattalin arzikin al’umma da samar da hanyoyin dogaro da kai, ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin tarayya ke aiwatar da manyan ayyukan raya ƙasa a Jihar Kaduna, ciki har da aikin gyaran hanyar Abuja–Kaduna–Zaria–Kano, hanyar Mando–Kaduna–Birnin Gwari, aikin bututun iskar gas na Kano zuwa Kaduna, da kuma ayyukan jirgin ƙasa da layin dogo na zamani.

Masu ruwa da tsaki da waɗanda suka ci gajiyar shirin sun yaba wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, bisa ayyukan raya ƙasa da suke aiwatarwa, inda suka bayyana cewa wadannan ayyuka za su taimaka wajen bunkasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’umma.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a wajen bikin yaye wadanda suka kammala horon da aka gudanar a makarantar Firamare da ke Rigachikun, jagoran Shirin Abdulmuminu Aminu Zaria, ya ce shirin wata alama ce ta jajircewar gwamnatin tarayya da ta jihar wajen samar wa jama’a damar dogaro da kai ta hanyar horar da su sana’o’i.

Ya bayyana cewa an horas da mahalarta shirin a fannoni daban-daban guda takwas tare da ba su tallafin kuɗi domin su fara ko kuma su faɗaɗa sana’o’insu.“Mun horas da su sana’o’i daban-daban tare da ba su tallafin kuɗi domin su zama masu dogaro da kansu kuma masu amfani ga al’umma,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

A nasa jawabin, Mai Kula da Shirin Renewed Hope Agenda a Jihar Kaduna, Abubakar Mohammed Mamadi, ya ce an kirkiri shirin ne domin bai wa mata da matasa ƙwarewa da kayan aikin da za su taimaka musu wajen samun ‘yancin tattalin arziki da kuma bayar da gudunmawa ga ci gaban al’umma.

Mamadi, wanda kuma shi ne mai ba Gwamnan Jihar Kaduna Shawara Kan Harkokin Siyasa, ya ce shirin ya yi daidai da manufofin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Tinubu da kuma hangen nesan gwamnatin Sanata Uba Sani na inganta rayuwar al’umma ta hanyar samar da ayyukan yi da shirye-shiryen tallafawa jama’a.

Ya buƙaci wadanda suka amfana da shirin da su yi amfani da damar da aka ba su yadda ya kamata, tare da ƙoƙarin zama masu ɗaukar ma’aikata maimakon jiran tallafin gwamnati kaɗai.

Ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa ayyukan ci gaba da yake gudanarwa a jihar, tare da gode wa dukkan mutanen da ƙungiyoyin da suka ba da gudunmawa wajen nasarar shirin.

Matasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • Sulaiman
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani
  • Sulaiman
    Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK
Matasa
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

MASU ALAKA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Next Post
Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.