ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

by Sulaiman and Shehu Yahaya
9 hours ago
Matasa

Matasa maza da Mata 1,200 ne suka amfana da horon sana’o’i da tallafin jari a ƙaramar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna karkashin shirin “Renewed Hope Empowerment Initiative” Na Shugaba Bola Tinubu da Gwamna Uba Sani.

Shirin, wanda aka gudanar domin inganta tattalin arzikin al’umma da samar da hanyoyin dogaro da kai, ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin tarayya ke aiwatar da manyan ayyukan raya ƙasa a Jihar Kaduna, ciki har da aikin gyaran hanyar Abuja–Kaduna–Zaria–Kano, hanyar Mando–Kaduna–Birnin Gwari, aikin bututun iskar gas na Kano zuwa Kaduna, da kuma ayyukan jirgin ƙasa da layin dogo na zamani.

Masu ruwa da tsaki da waɗanda suka ci gajiyar shirin sun yaba wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, bisa ayyukan raya ƙasa da suke aiwatarwa, inda suka bayyana cewa wadannan ayyuka za su taimaka wajen bunkasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’umma.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a wajen bikin yaye wadanda suka kammala horon da aka gudanar a makarantar Firamare da ke Rigachikun, jagoran Shirin Abdulmuminu Aminu Zaria, ya ce shirin wata alama ce ta jajircewar gwamnatin tarayya da ta jihar wajen samar wa jama’a damar dogaro da kai ta hanyar horar da su sana’o’i.

Ya bayyana cewa an horas da mahalarta shirin a fannoni daban-daban guda takwas tare da ba su tallafin kuɗi domin su fara ko kuma su faɗaɗa sana’o’insu.“Mun horas da su sana’o’i daban-daban tare da ba su tallafin kuɗi domin su zama masu dogaro da kansu kuma masu amfani ga al’umma,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

A nasa jawabin, Mai Kula da Shirin Renewed Hope Agenda a Jihar Kaduna, Abubakar Mohammed Mamadi, ya ce an kirkiri shirin ne domin bai wa mata da matasa ƙwarewa da kayan aikin da za su taimaka musu wajen samun ‘yancin tattalin arziki da kuma bayar da gudunmawa ga ci gaban al’umma.

Mamadi, wanda kuma shi ne mai ba Gwamnan Jihar Kaduna Shawara Kan Harkokin Siyasa, ya ce shirin ya yi daidai da manufofin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Tinubu da kuma hangen nesan gwamnatin Sanata Uba Sani na inganta rayuwar al’umma ta hanyar samar da ayyukan yi da shirye-shiryen tallafawa jama’a.

Ya buƙaci wadanda suka amfana da shirin da su yi amfani da damar da aka ba su yadda ya kamata, tare da ƙoƙarin zama masu ɗaukar ma’aikata maimakon jiran tallafin gwamnati kaɗai.

Ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa ayyukan ci gaba da yake gudanarwa a jihar, tare da gode wa dukkan mutanen da ƙungiyoyin da suka ba da gudunmawa wajen nasarar shirin.

Matasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC
  • Sulaiman
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Sulaiman
    Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping
  • Sulaiman
    Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping
Matasa
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna

MASU ALAKA

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni
Manyan Labarai

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.