Matasa maza da Mata 1,200 ne suka amfana da horon sana’o’i da tallafin jari a ƙaramar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna karkashin shirin “Renewed Hope Empowerment Initiative” Na Shugaba Bola Tinubu da Gwamna Uba Sani.
Shirin, wanda aka gudanar domin inganta tattalin arzikin al’umma da samar da hanyoyin dogaro da kai, ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin tarayya ke aiwatar da manyan ayyukan raya ƙasa a Jihar Kaduna, ciki har da aikin gyaran hanyar Abuja–Kaduna–Zaria–Kano, hanyar Mando–Kaduna–Birnin Gwari, aikin bututun iskar gas na Kano zuwa Kaduna, da kuma ayyukan jirgin ƙasa da layin dogo na zamani.
Masu ruwa da tsaki da waɗanda suka ci gajiyar shirin sun yaba wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, bisa ayyukan raya ƙasa da suke aiwatarwa, inda suka bayyana cewa wadannan ayyuka za su taimaka wajen bunkasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’umma.
Da yake jawabi a wajen bikin yaye wadanda suka kammala horon da aka gudanar a makarantar Firamare da ke Rigachikun, jagoran Shirin Abdulmuminu Aminu Zaria, ya ce shirin wata alama ce ta jajircewar gwamnatin tarayya da ta jihar wajen samar wa jama’a damar dogaro da kai ta hanyar horar da su sana’o’i.
Ya bayyana cewa an horas da mahalarta shirin a fannoni daban-daban guda takwas tare da ba su tallafin kuɗi domin su fara ko kuma su faɗaɗa sana’o’insu.“Mun horas da su sana’o’i daban-daban tare da ba su tallafin kuɗi domin su zama masu dogaro da kansu kuma masu amfani ga al’umma,” in ji shi.
A nasa jawabin, Mai Kula da Shirin Renewed Hope Agenda a Jihar Kaduna, Abubakar Mohammed Mamadi, ya ce an kirkiri shirin ne domin bai wa mata da matasa ƙwarewa da kayan aikin da za su taimaka musu wajen samun ‘yancin tattalin arziki da kuma bayar da gudunmawa ga ci gaban al’umma.
Mamadi, wanda kuma shi ne mai ba Gwamnan Jihar Kaduna Shawara Kan Harkokin Siyasa, ya ce shirin ya yi daidai da manufofin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Tinubu da kuma hangen nesan gwamnatin Sanata Uba Sani na inganta rayuwar al’umma ta hanyar samar da ayyukan yi da shirye-shiryen tallafawa jama’a.
Ya buƙaci wadanda suka amfana da shirin da su yi amfani da damar da aka ba su yadda ya kamata, tare da ƙoƙarin zama masu ɗaukar ma’aikata maimakon jiran tallafin gwamnati kaɗai.
Ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa ayyukan ci gaba da yake gudanarwa a jihar, tare da gode wa dukkan mutanen da ƙungiyoyin da suka ba da gudunmawa wajen nasarar shirin.















Discussion about this post