‘Yan Majalisar Wakilai shida daga Jihar Oyo sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa APM.
An sanar da sauya sheƙar tasu ne a ranar Talata yayin zaman majalisar bayan hutun Sallah.
Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya karanta wasiƙun da ‘yan majalisar suka aike domin sanar da majalisar matakin da suka ɗauka.
‘Yan majalisar da suka sauya sheƙar sun haɗa da Anthony Adebayo Adepoju, Adedeji Stanley Olajide, Makanjuola Sunday Ojo, Najimdeen Oyeshina Oyedeji, Folajimi Oyekunle da Abass Adekunle Adigun.
Sauya sheƙar tasu na zuwa ne makonni kaɗan bayan Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya koma jam’iyyar APM kuma ya zama ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen shekarar 2027.
A zaman majalisar, jagoran marasa rinjaye na Majalisar Wakilai, Kingsley Chinda, shi ma ya sanar da ficewarsa daga PDP zuwa APC tare da yin murabus daga muƙaminsa.















Discussion about this post