’Yan takarar gwamna na jam’iyyar ADC a jihohin Arewa maso Yamma bakwai sun yi alƙawarin biyan ma’aikata mafi ƙarancin albashi na Naira 110,000 idan aka zaɓe su a shekarar 2027.
’Yan takarar sun yi alƙawarin ne ranar Laraba a Abuja, lokacin da suka sanya hannu kan wata yarjejeniya ta haɗin gwiwa kan tsaro, ilimi da ci gaban yankin.
Sun kuma yi alƙawarin samar sa asibitocin ƙwararru guda 21, wato asibiti ɗaya a kowace mazaɓar Sanatoci, tare da ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro da ilimi.
’Yan takarar sun ce za su yi amfani da jirage marasa matuƙa, na’urorin sa ido wajen yaƙi da ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane.
Za su kuma kafa Cibiyar Haɗa Tsaron Yankin Arewa maso Yamma.
Da yake magana bayan sanya hannu kan yarjejeniyar, ɗan takarar ADC na Jihar Kebbi kuma tsohon Antoni-Janar na Tarayya, Abubakar Malami, ya ce Arewa maso Yamma tana fuskantar matsaloli masu yawa sakamakon rashin tsaro, talauci da ƙarancin ayyukan gwamnati.
’Yan takarar sun zargi gwamnatocin APC da rashin amfani da kuɗaɗen gwamnati, suna cewa al’ummar yankin ba su samu ci gaba ba duk da yawan kuɗaɗen da jihohin ke samu daga gwamnatin tarayya.
Sun yi alƙawarin inganta noma, kiwon lafiya, ilimi, hanyoyi, wutar lantarki, samar da ruwa da kasuwanci tsakanin jihohin yankin idan aka zaɓe su.
’Yan takarar ADC sun kuma yi alƙawarin yin aiki tare wajen magance matsalolin da suka shafi jihohi da dama, yayin da kowace jiha za ta ci gaba da kula da gwamnatinta da kasafinta.














