Kamfanin ba da shawara kan batun tattalin arziki na BCG, ya gabatar da wani rahoto a kwanan baya, wanda ya nuna cewa, ya zuwa karshen shekarar 2025, yawan jarin ketare da ake adanawa da kula da su a yankin Hong Kong na kasar Sin, ya kai dalar Amurka tiriliyan 2 da biliyan 950, adadin da ya zarce na kasar Switzerland.
Hakan ya nuna cewa, yankin Hong Kong ya riga ya zama cibiyar kula da jarin ketare mafi girma a duniya.
A ganin jami’ai da masana na yankin Hong Kong, dalilin da ya sa yankin samun wannan matsayi, shi ne manufar da ake aiwatarwa a yankin, ta “kasa daya, tsarin mulki biyu”.
A bisa wannan manufa, jari zai iya shiga da fita daga yankin cikin ‘yanci, kana an bayyana dukkan ka’idoji a fili, saboda haka ana cikin wani yanayi na tabbas wajen samun riba ta hanyar zuba jari.
Haka zalika, yankin Hong Kong ya kasance “kofar kasar Sin a fannin hada-hadar kudi”, inda yake samar da dimbin damammaki na zuba jari, a kasuwannin babban yankin kasar Sin ga ‘yan kasuwar kasashe daban daban.Ban da haka, an ce yankin Hong Kong na kokarin taka rawa, a matsayin “kofar yankin Asiya da tekun Pasifika”, inda yake amfani da dimbin kwararru da yake da su a fannonin hada-hadar kudi, da shari’a, da jigilar kaya, da kimiyya da fasaha, wajen zurfafa hadin gwiwar sassan kasa da kasa ta fuskar tattalin arziki, tare da samar da gudunmawa ga bangaren ayyuka na kasar Sin, na bude kofarta ga duniya ta wata ingantacciyar hanya. (Bello Wang)















Discussion about this post