Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 3 ga Yuni, 2026 domin sauraron ƙarar da tsohon mataimakin shugaban ADC, Nafiu Bala Gombe, ya shigar yana ƙalubalantar shugabancin David Mark da Rauf Aregbesola a jam’iyyar.
An ruwaito cewa an mayar da ƙarar zuwa gaban Mai Shari’a Peter Lifu bayan an ɗaga Mai Shari’a Emeka Nwite zuwa Kotun Ɗaukaka Ƙara. Nafiu Bala na neman kotu ta hana David Mark, da Aregbesola da sauran mambobin kwamitin riƙon ƙwarya na jam’iyyar ci gaba da bayyana kansu a matsayin shugabannin ADC.
Mai ƙarar ya yi zargin cewa yadda aka kafa sabon shugabancin jam’iyyar ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ADC da kuma dokokin zaɓe.
A cikin ƙarar, ya haɗa da ADC, da David Mark, da Rauf Aregbesola, da INEC da tsohon shugaban jam’iyyar, Ralph Nwosu a matsayin waɗanda ake kara.
Tun da farko, Kotun Ƙoli ta umarci a ci gaba da sauraron shari’ar a Babbar Kotun Tarayya bayan ta soke wani umarni da ya dakatar da ci gaban ƙarar. Haka kuma, INEC ta dawo da sunayen shugabannin ɓangaren David Mark a shafinta bayan hukuncin kotun ƙoli.















Discussion about this post