ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Sara-Suka 7 Da Suka Addabi Jama’an Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
'Yan sara-suka

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta cafke matasa bakwai (7) bisa zarginsu da kasance ‘yan daban da suke addabar jama’a da aka fi saninsu da ‘yan Sara-Suka.

 

A wata sanarwar da Kakakin hukumar ‘yansandan jihar Sufuritendan Ahmed Mohammed Wakil ya fitar a ranar Lahadi na cewa, bincike ya nuna cewa wadanda aka kaman ana zarginsu ne da kasance ‘yan kungiyar dabanci da ake kira da ‘Sara-Suka’ wadanda suka addabi al’ummar cikin kwaryar Bauchi.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

A cewarsa wannan matakin ya biyo bayan umarnin da kwamishinan ‘yansandan jihar ya bai wa kwamandojin yanki-yanki, DPOs da jami’an dakile bata-gari da su tabbatar sun kutsa kai lunguna da sakona na maboyar ‘yan ta’adda domin tabbatar da an gudanar da bikin Ista cikin kwanciyar hankali a fadin jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A fadinsa, a ranar 08/04/2023 jami’ansu da hadin guiwar wasu jami’an tsaron sun samu rahoton sirri inda suka yi dirar mikiya ga maboyar ‘yan daban da ke cikin wata ginin da ba a kammala ginawa a unguwar Magaji Quarters tare da taso keyar matasan.

 

Wadanda aka kama din su ne: Rayyanu Mohammed Dan shekara (25) Mustapha Harisu (19); Yusuf Ibrahim (Mai shekara 18); Mubarak Lawal (18); Abubakar Musa (18); Al-Amin Hussaini (20); da kuma Hamza Umar (17) dukkaninsu mazauna Magaji quarters Bauchi.

 

A kan haka, an kwato makamai iri-iri da wasu abubuwan sha daga hannunsu yayin farmakin da suka hada da gatari guda biyu; wukake uku; kwalabe goma mara komai na maganin tari da ke sanya maye; kunshi daya na tabar wiwi da dai sauransu.

 

Sanarwar ta kara da cewa, bincike na cigaba da gudana kuma za su kara zafafa bincikensu kan lamarin, bayan sun kammala kuma za su gurfanar da su a gaban kuliya mance sabo.

 

Wakil ya kara da cewa kwamishinan ‘yansandan jihar CP Aminu Alhassan ya shawarci iyayen da suke sanya ido kan harkokin ‘ya’yansu domin karesu daga fadawa munanan ayyuka.

'Yan sara-suka
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Wani Dan Amurka Dauke Da Kullin Hodar Iblis 117

NDLEA Ta Cafke Wani Dan Amurka Dauke Da Kullin Hodar Iblis 117

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.