Jami’an Rundunar ’Yansandan Nijeriya sun ceto mutane 75 da suka hada da maza, mata da yara, bayan wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da su daga motocin haya a Karamar Hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna.
An ce wadanda lamarin ya rutsa da su, wadanda ake zargin matafiya ne Fulani, an tare su ne a ranar 19 ga Agusta, 2026, da misalin karfe 5:30 na yamma, lokacin da wasu ’yan bindiga dauke da bindigogin AK-47 da wasu manyan makamai suka kai musu farmaki a kauyen Folwaya, kusa da Birnin Gwari.
Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ’Yansandan Nijeriya, CSP Anietie Iniedu, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, “Rahotanni sun nuna cewa maharan sun tilasta wa fasinjojin shiga cikin daji, inda suka boye su a cikin wani kogo da ke wani yanki mai Duwatsu.
“Amma, da isar jami’an tsaron, bayan Rundunar ’Yansandan Jihar Kaduna ta samu sahihin bayani daga reshen Birnin Gwari na Kungiyar Masu Kula da Sufurin Mota ta Kasa (NURTW). Nan take, bisa bayanan sirrin da aka samu, aka tura wata tawagar musamman daga Ofishin ’Yansanda na Yankin Birnin Gwari zuwa wurin da ake zargin an ɓoye mutanen.
“Jami’an ’yansandan, sun kutsa cikin yankin da manyan makamanau, lamarin da ya tilasta wa masu garkuwa da mutanen tserewa tare da barin wadanda suka yi garkuwa da su. An samu nasarar ceto dukkan mutane 75 ba tare da wani rauni ba.”
Da yake yabawa jami’an bisa nasarar aikin, Kwamishinan ’Yansandan Jihar Kaduna, CP Rabiu Muhammad, ya yaba wa reshen NURTW na Birnin Gwari bisa samar da bayanan sirri cikin gaggawa.
Ya bayyana hadin kan jama’a da jami’an tsaro a matsayin muhimmin ginshiki wajen yaki da satar mutane da sauran manyan laifuka.














