Da yammacin yau Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna da sarkin masarautar Hashemite ta Jordan, Abdullah II Bin Hussein, wanda ke ziyarar aiki a Sin a babban dakin taron jama’a dake nan birnin Beijing. Shugabannin kasashen biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya.
Xi ya jaddada cewa Sin tana goyon bayan tsagaita bude wuta a dukkan fannoni da kuma warware takaddama ta hanyar siyasa da diflomasiyya.
Ya ce batun Falasdinu shi ne ginshikin matsalar Gabas ta Tsakiya, kuma ya kamata a inganta warware matsalar ta hanyar bin ka’idoji guda hudu, na farko, dole a warware matsalar ta hanyar siyasa, na biyu, dole ne a tabbatar da “’yan Falasdinu sun shugabancin kasarsu”, na uku, dole ne a tabbatar da ra’ayin jin kai, na hudu kuma, dole ne a tabbatar da adalci.
A nasa bangare, Abdullah II Bin Hussein ya bayyana cewa, Jordan ta yaba da matsayin Sin mai adalci kan harkokin Gabas ta Tsakiya da kuma goyon bayanta ga harkokin tabbatar da adalci ga kasashen Larabawa, wanda ke da matukar muhimmanci ga kasashen yankin.(Safiyah Ma)














