Rundunar ‘Yansandan Babban Birnin Tarayya (FCT) ta sanar a ranar Laraba cewa ta kama mutane 14 da ake zargi da satar motoci, da ‘yan fashi, tare da kwato motoci 17 da aka sace a sassa daban-daban na Abuja.
Da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar rundunar, Kwamishinan ‘Yansanda, Ahmed Sanusi, ya bayyana cewa kamen ya biyo bayan ƙara ƙaimin gudanar da ayyukan sirri na leƙen asiri da aka fara tun daga watan Maris 2026 zuwa yanzu.
Ya ce an gudanar da waɗannan ayyuka ne ta hannun sassa daban-daban na rundunar da suka haɗa da Mabushi, Durumi, Maitama, da Babban Ofishin ‘Yansanda na FCT, inda aka mayar da hankali kan satar motoci, fashin “one chance”, da sauran laifuka masu alaƙa.
Sanusi ya ƙara da cewa, ana zargin waɗannan mutane da hannu a kwacen motoci da amfani da bindiga, satar motoci daga wuraren ajiye su, da kuma masu amfani da motocin wajen aikata laifuka.













Discussion about this post