Rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi ta kama mutane bakwai da ake zargin ‘yan bindiga neyayin wani samame da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Bagudo.
A cikin wata sanarwa da kakakin ‘yansandan jihar, SP Bashir Usman, ya fitar, an ce an kama mutanen ne a ranar 5 ga watan Yuni, 2026, a wani aiki da aka gudanar da bayanan sirri a dajin Soda da kuma ƙauyukan da ke kan iyakar jihar.
‘Yansanda sun ce an kama wasu uku a kan babur a hanyar Illo–Lolo, inda ake zargin suna kai wa ‘yan bindiga abinci a cikin daji.
An kuma ƙwato babur ɗin da suke amfani da shi.
A wani samame na daban a yankin Bakin Ruwa–Ka’oje, an kama wasu mutum huɗu a wani ƙoƙari na ƙara matsin lamba kan masu aikata laifuka a yankin.
Ana ci gaba da bincike kan waɗanda ake zargin, ciki har da yiwuwar alaƙarsu da harin da aka kai wanda ya yi sanadin mutuwar jami’an FRSC uku.
Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kebbi, Umar Hadejia, ya bayyana kamen a matsayin babban nasara a yaƙi da ‘yan bindiga.
Ya kuma yaba wa jami’an tsaro tare da gode wa jama’a bisa bayar da bayanan da suka taimaka.
Rundunar ta ce za a gurfanar da waɗanda ake zargin a kotu bayan kammala bincike.














Discussion about this post