Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya ce ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Mohammed Hayatu-Deen, ya fi Atiku Abubakar ƙwarewa.
Da yake magana a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, Lawal ya ce Atiku da Hayatu-Deen ba a mataki ɗaya suke ba wajen ƙwarewa da gogewa.
Ya bayyana cewa Hayatu-Deen na da ƙwarewa sosai a fannin tattalin arziƙi, ciki har da lokacin da ya jagoranci ƙungiyar Nigerian Economic Summit Group (NESG).
“Hayatu-Deen ya fi Atiku ƙwarewa. Ba a mataki ɗaya sukw ba,” in ji Lawal.
Dukaninsu sun shiga zaɓen fidda-gwani na ADC domin takarar shugaban ƙasa a 2027.
Atiku ya lashe zaɓen, yayin da Hayatu-Deen ya zo na uku.















Discussion about this post