Mambobi 17 na Majalisar Wakilai ta Tarayya sun fice daga Jam’iyyar ADC zuwa NDC.
An sanar da ficewar tasu ne a zauren majalisar yayin zaman majalisa na ranar Talata.
Wannan na zuwa ne bayan a ranar Litinin, Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso su ma suka fice daga ADC zuwa NDC, a wani lamarin da ke ƙara sauya yanayin siyasar zaɓen 2027.
Daga cikin ‘yan majalisar da suka koma NDC akwai Yusuf Datti, Uchenna Okonkwo, Adamu Wakili, Thaddeus Attah, George Ozodinobi, Lilian Orogbu, Oluwaseyi Sowunmi, Peter Aniekwe, Mukhtar Zakari, George Oluwande da Munachim Umezuruike.
Sauran sun haɗa da Emeka Idu, Jesse Onuakalusi, Ifeanyi Uzokwe, Afam Ogene da Abdulhakeem Ado.Cikakken labari na nan tafe…















Discussion about this post