ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Hunan

Da safiyar yau Laraba, ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai. Yayin taron, mai ba da taimako ga ministan kasuwanci na kasar Sin Tang Wenhong, da mataimakin gwamnan lardin Hunan Wang Junshou, sun gabatar da batutuwa masu nasaba da baje kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka karo na 4 da za a shirya a birnin Changsha, tare da amsa tambayoyin manema labarai.

Bisa gabatarwar da Mr. Tang Wenhong ya yi, za a gudanar da baje kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka karo na 4 daga ranar 12 zuwa 15 ga watan Yuni a birnin Changsha dake lardin Hunan, kuma jigonsa shi ne “Sin da kasashen Afirka suna himmatuwa wajen cimma zamanantarwa”, taron da gwamnatin lardin Hunan da ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin za su dauki nauyin shiryawa tare. Taron daya ne daga cikin muhimman ayyukan mu’amalar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka a bana.

  • Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho
  • ‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Sojoji Da ‘Yan Siyasa Wajen Samun Bayanan Sirri – Zulum 

A cikin ’yan shekarun nan, bisa manyan tsare-tsare na shugabannin kasashen Sin da Afirka, hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Afirka ya samu sabon ci gaba. Musamman a gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a birnin Beijing a watan Satumban bara, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana matakai a aikace na “Ayyuka guda 10”, a fannin hadin gwiwa tare da kasashen Afirka, wadanda suka sa kaimi ga hadin gwiwar Sin da Afirka.

ADVERTISEMENT

A shekarar 2024, adadin ciniki tsakanin Sin da Afirka ya kai dalar Amurka biliyan 295.6, wanda ya karu da kashi 4.8 bisa dari idan aka kwatanta da makamancin lokaci na shekarar 2023, wanda hakan ya kafa sabon tarihi a shekara ta hudu a jere.

Kasar Sin ta kasance abokiyar cinikayya mafi girma ta kasashen Afirka cikin tsawon shekaru 16 a jere. Daga cikinsu, darajar kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga Afirka sun kai dalar Amurka biliyan 116.8, adadin da ya karu da kashi 6.9 bisa dari, sannan kayayyakin da take fitarwa zuwa Afirka ya kai darajar dalar Amurka biliyan 178.8, wanda ya karu da kashi 3.5 bisa dari. (Safiyah Ma)

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Hunan
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea
Hunan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

MASU ALAKA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Next Post
Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo

Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.