ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kammala Hanyar Kano Zuwa Katsina Da Gadar Legas A Kan Naira Biliyan 493 – Minista

by Sulaiman
11 months ago
Legas

Gwamnatin Tarayya ta kasafta jimillar naira biliyan 493 domin wasu muhimman ayyuka biyu: kammala hanyar Kano zuwa Katsina mai tsawon kilomita 152 da kuma gina sabuwar Gadar Carter a Jihar Legas.

 

Ministan Ayyuka, David Umahi, shi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa jim kaɗan bayan taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta a ranar Laraba, 13 ga Agusta, 2025.

ADVERTISEMENT
  • Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya
  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici

Ministan ya ce an yi babban ƙari a kuɗin aikin hanyar Kano zuwa Katsina saboda yanayin tattalin arziki da ake ciki.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar da Matatar Sarrafa Ma’adanin Lithium Ta $200m A Zamfara

Umahi ya ce a da, gwamnatin da ta gabata ta raba aikin hanyar ne gida biyu.

 

Ya ce: “Sashe na Ɗaya, mai tsawon kilomita 74.1, da farko an ba da kwangilar sa ne a cikin 2013 a kan kuɗi naira biliyan 14, aka ƙara shi zuwa naira biliyan 24. To yanzu kuma an ƙara shi zuwa naira biliyan 68.

 

“Sashe na Biyu, mai tsawon kilomita 79.5 da aka bayar a cikin 2019 a kan kuɗi naira biliyan 29, aka ƙara shi zuwa naira biliyan 46, yanzu kuma ya koma naira biliyan 66.115.”

 

Jimillar kuɗin ayyukan a yanzu shi ne kimanin naira biliyan 134, sannan aka kasafta naira biliyan 6 a Kasafin Kuɗin shekarar 2024 da naira biliyan 34 a Kasafin Kuɗin 2025 don Sashe na Ɗaya. Shi kuma Sashe na Biyu an ware masa naira biliyan 80 a tsawon waɗannan shekaru biyu.

 

A game da Gadar Carter kuwa, Umahi ya ce daga binciken ƙarƙashin ruwa da aka gudanar a shekarun 2013 da 2019, an gano cewa masu haƙar ma’adinai ba bisa doka ba da kuma zaizayar ƙasa sun yi wa jikin gadar da turakun ta lahani sosai.

 

Kamfanin Julius Berger, wanda shi ne ke da alhakin yi wa gadar gyara a ƙarƙashin ruwa da tuwasun ta, ya ba da shawarar cewa gadar ta wuce a ceto ta, abin da ya kamata kawai shi ne a sake gina ta baki ɗaya.

 

Ita dai Gadar Carter, an gina ta ne a cikin 1901, kuma tana daga cikin manyan gadoji uku da suka haɗa Tsibirin Legas (wato Island) da babban garin Legas. Sauran su ne Gadar Third Mainland da Gadar Eko.

 

An raɗa mata sunan Sir Gilbert Thomas Carter ne, wani gwamnan Legas na zamanin mulkin mallaka.

 

An sha yi mata gyare-gyare bayan samun mulkin kai, domin a shekarun 1970 ma sai da aka kwance ta gaba ɗaya sannan aka sake haɗa ta.

Legas
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Nazarin Tattalin Arziki Tare Da Masana Da ‘Yan Kasuwa
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar da Matatar Sarrafa Ma’adanin Lithium Ta $200m A Zamfara
  • Sulaiman
    Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

July 13, 2026
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar da Matatar Sarrafa Ma’adanin Lithium Ta $200m A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar da Matatar Sarrafa Ma’adanin Lithium Ta $200m A Zamfara

July 13, 2026
Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa
Manyan Labarai

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

July 13, 2026
Next Post
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Jerin Ayyuka Karo Na Uku A Wajen Kumbon

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Jerin Ayyuka Karo Na Uku A Wajen Kumbon

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Nazarin Tattalin Arziki Tare Da Masana Da ‘Yan Kasuwa

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Nazarin Tattalin Arziki Tare Da Masana Da ‘Yan Kasuwa

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

July 13, 2026
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar da Matatar Sarrafa Ma’adanin Lithium Ta $200m A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar da Matatar Sarrafa Ma’adanin Lithium Ta $200m A Zamfara

July 13, 2026
Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

July 13, 2026
Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.