ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kammala Hanyar Kano Zuwa Katsina Da Gadar Legas A Kan Naira Biliyan 493 – Minista

by Sulaiman
10 months ago
Legas

Gwamnatin Tarayya ta kasafta jimillar naira biliyan 493 domin wasu muhimman ayyuka biyu: kammala hanyar Kano zuwa Katsina mai tsawon kilomita 152 da kuma gina sabuwar Gadar Carter a Jihar Legas.

 

Ministan Ayyuka, David Umahi, shi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa jim kaɗan bayan taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta a ranar Laraba, 13 ga Agusta, 2025.

ADVERTISEMENT
  • Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya
  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici

Ministan ya ce an yi babban ƙari a kuɗin aikin hanyar Kano zuwa Katsina saboda yanayin tattalin arziki da ake ciki.

 

LABARAI MASU NASABA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Umahi ya ce a da, gwamnatin da ta gabata ta raba aikin hanyar ne gida biyu.

 

Ya ce: “Sashe na Ɗaya, mai tsawon kilomita 74.1, da farko an ba da kwangilar sa ne a cikin 2013 a kan kuɗi naira biliyan 14, aka ƙara shi zuwa naira biliyan 24. To yanzu kuma an ƙara shi zuwa naira biliyan 68.

 

“Sashe na Biyu, mai tsawon kilomita 79.5 da aka bayar a cikin 2019 a kan kuɗi naira biliyan 29, aka ƙara shi zuwa naira biliyan 46, yanzu kuma ya koma naira biliyan 66.115.”

 

Jimillar kuɗin ayyukan a yanzu shi ne kimanin naira biliyan 134, sannan aka kasafta naira biliyan 6 a Kasafin Kuɗin shekarar 2024 da naira biliyan 34 a Kasafin Kuɗin 2025 don Sashe na Ɗaya. Shi kuma Sashe na Biyu an ware masa naira biliyan 80 a tsawon waɗannan shekaru biyu.

 

A game da Gadar Carter kuwa, Umahi ya ce daga binciken ƙarƙashin ruwa da aka gudanar a shekarun 2013 da 2019, an gano cewa masu haƙar ma’adinai ba bisa doka ba da kuma zaizayar ƙasa sun yi wa jikin gadar da turakun ta lahani sosai.

 

Kamfanin Julius Berger, wanda shi ne ke da alhakin yi wa gadar gyara a ƙarƙashin ruwa da tuwasun ta, ya ba da shawarar cewa gadar ta wuce a ceto ta, abin da ya kamata kawai shi ne a sake gina ta baki ɗaya.

 

Ita dai Gadar Carter, an gina ta ne a cikin 1901, kuma tana daga cikin manyan gadoji uku da suka haɗa Tsibirin Legas (wato Island) da babban garin Legas. Sauran su ne Gadar Third Mainland da Gadar Eko.

 

An raɗa mata sunan Sir Gilbert Thomas Carter ne, wani gwamnan Legas na zamanin mulkin mallaka.

 

An sha yi mata gyare-gyare bayan samun mulkin kai, domin a shekarun 1970 ma sai da aka kwance ta gaba ɗaya sannan aka sake haɗa ta.

Legas
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • Sulaiman
    Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

MASU ALAKA

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki
Labarai

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi
Labarai

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Next Post
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Jerin Ayyuka Karo Na Uku A Wajen Kumbon

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Jerin Ayyuka Karo Na Uku A Wajen Kumbon

LABARAI MASU NASABA

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

Sowore Ya Yi Kira Ga Zanga-Zangar Kasa Kan Tinubu Ranar Litinin

June 14, 2026
Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

Shugaban Mongoliya Ya Zanta Da Ministan Wajen Kasar Sin

June 14, 2026
Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

Ƴansanda Sun Kunce Bam Ɗin Da ƴan Bindiga Suka Dasa A Zamfara

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.