• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Karfafawa Karin Kamfanonin Kasar Sin Gwiwar Zuba Jari A Nahiyar Afrika

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Za A Karfafawa Karin Kamfanonin Kasar Sin Gwiwar Zuba Jari A Nahiyar Afrika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar bunkasa zuba jari a nahiyar Afrika ta kasar Sin (CABC), ta kaddamar da rahoto kan jarin da kamfanonin kasar Sin suka zuba a nahiyar Afrika na 2024. 

 

Rahoton wanda aka kaddamar da yammacin jiya Juma’a, ya bayyana nasarorin da aka samu da sabbin bangarori da ma damarmakin zuba jari dake akwai a kasashen Afrika.

  • Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar
  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Sadarwa

A kan fitar da rahoton a kowacce shekara tun daga shekarar 2021. Wannan sakamako ne na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika FOCAC, karkashin jadawalin aikin da ake son gudanarwa daga 2021-2024, wanda aka fitar a Dakar na kasar Senegal. Kuma a bana, rahoton na zuwa ne gabanin taron na FOCAC wanda za a yi a Beijing, daga ranar 4 zuwa 6 ga watan Satumba mai zuwa.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

A jawabinsa na bude taron, babban shugaban majalisar CABC, Wang Xiaoyong ya bayyana dandalin FOCAC a matsayin wata kadara mai daraja ga Sin da Afirka.

 

Yana mai cewa, sun yi ammana cikin shekaru 3 masu zuwa, karkashin dabaru daga gwamnatocin Sin da Afirka, da goyon baya daga bangarorin diplomasiyya da cinikayya da hada-hadar kudi, hadin gwiwar Sin da Afrika a bangarorin tattalin arziki da cinikayya da zuba jari, zai kai ga zamanantar da nahiyar Afrika.

 

A cewar rahoton, zuwa karshen shekarar 2022, jarin da Sin ta zuba kai tsaye a nahiyar Afrika ya zarce dala biliyan 47, kuma sama da kamfanonin Sin 3,000 ne suka zuba jari tare da gudanar da harkokin kasuwanci a Afrika. kana a rabin farko na shekarar 2023, jarin kai tsaye na Sin a Afrika ya zarce dala biliyan 1.82, wanda ya karu da kaso 4.4 a kowacce shekara.

 

Rahoton ya kara da cewa, kasar Sin na kara yawan jarinta a Afrika a bangarori daban daban, inda ta kara fadadawa zuwa bangarorin masu tasowa kamar na tattalin arzikin dijital da ayyukan masu kare muhalli da sufurin sama da hidimomin kudi da cinikayya ta yanar gizo da sauransu.

 

Bugu da kari, rahoton ya ce ta hanyar zuba jari dake mayar da hankali ga harkokin kasuwanci, jarin Sin kan ababen more rayuwa da sauran sabbin bangarori suna bunkasa tsarin ayyukan masana’atu da ma daukaka darajarsu.

 

Da yake jawabi, tsohon ministan kudi da tsare-tsare na kasar Habasha kuma mai neman digirin-digirgir a cibiyar nazarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa a jami’ar Peking ta kasar Sin Endalkachew Sime, ya bayyana rahoton a matsayin mai muhimmanci wajen tsara dabaru da manufofi, saboda yadda ya yi bayani dalla-dalla kan bangarorin hadin gwiwa da wadanda ya kamata a mayar da hankali kan su, da ma kalubalen da ake fuskanta. Haka kuma zai kara aminci tsakanin bangarorin biyu da kyautata muhallin hadin gwiwa.

 

Shi kuwa masanin tattalin arziki kuma tsohon ma’aikacin bankin duniya kuma mashawarcin shugaban kasar Kenya kan harkokin tattalin arziki, Dr. Mwangi Wachira, cewa ya yi, yayin da kasashen nahiyar Afrika ke kokarin neman ci gaba, kasar Sin ta tallafawa wannan kokari ta hanyar gudanar da ayyukan da suka taimaka wajen magance tushen manyan kalubalen nahiyar.

 

Ya ce ana samun nasarar hadin gwiwar bangarorin biyu ne saboda manufofin Sin a bayyane suke, kuma tana taimakawa ba tare da kakaba akidunta kan su ba, wato tana taimakawa wajen zamanantar da Afrika, ta hanyar da ta dace da Afrika.

 

Rahoton ya ce za a kara karfafawa kamfanonin Sin gwiwar zubawa da fada jarinsu a kasashen Afrika, tare da kira ga gwamnatocin nahiyar Afrika su kyautata muhallin kasuwanci da inganta dangantakar Sin da Afrika. (Fa’iza Mustapha)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Lokutan, Sai Mun Ranci Kudin Mota Domin Komawa Gida Bayan Daukar Fim –Ciroki

Next Post

Yadda Ake Miyar Tafasa Ta Gargajiya

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

4 hours ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

5 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

6 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

7 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

8 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

9 hours ago
Next Post
Yadda Ake Miyar Tafasa Ta Gargajiya

Yadda Ake Miyar Tafasa Ta Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.