ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Karfafawa Karin Kamfanonin Kasar Sin Gwiwar Zuba Jari A Nahiyar Afrika

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afrika

Cibiyar bunkasa zuba jari a nahiyar Afrika ta kasar Sin (CABC), ta kaddamar da rahoto kan jarin da kamfanonin kasar Sin suka zuba a nahiyar Afrika na 2024. 

 

Rahoton wanda aka kaddamar da yammacin jiya Juma’a, ya bayyana nasarorin da aka samu da sabbin bangarori da ma damarmakin zuba jari dake akwai a kasashen Afrika.

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar
  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Sadarwa

A kan fitar da rahoton a kowacce shekara tun daga shekarar 2021. Wannan sakamako ne na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika FOCAC, karkashin jadawalin aikin da ake son gudanarwa daga 2021-2024, wanda aka fitar a Dakar na kasar Senegal. Kuma a bana, rahoton na zuwa ne gabanin taron na FOCAC wanda za a yi a Beijing, daga ranar 4 zuwa 6 ga watan Satumba mai zuwa.

 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

A jawabinsa na bude taron, babban shugaban majalisar CABC, Wang Xiaoyong ya bayyana dandalin FOCAC a matsayin wata kadara mai daraja ga Sin da Afirka.

 

Yana mai cewa, sun yi ammana cikin shekaru 3 masu zuwa, karkashin dabaru daga gwamnatocin Sin da Afirka, da goyon baya daga bangarorin diplomasiyya da cinikayya da hada-hadar kudi, hadin gwiwar Sin da Afrika a bangarorin tattalin arziki da cinikayya da zuba jari, zai kai ga zamanantar da nahiyar Afrika.

 

A cewar rahoton, zuwa karshen shekarar 2022, jarin da Sin ta zuba kai tsaye a nahiyar Afrika ya zarce dala biliyan 47, kuma sama da kamfanonin Sin 3,000 ne suka zuba jari tare da gudanar da harkokin kasuwanci a Afrika. kana a rabin farko na shekarar 2023, jarin kai tsaye na Sin a Afrika ya zarce dala biliyan 1.82, wanda ya karu da kaso 4.4 a kowacce shekara.

 

Rahoton ya kara da cewa, kasar Sin na kara yawan jarinta a Afrika a bangarori daban daban, inda ta kara fadadawa zuwa bangarorin masu tasowa kamar na tattalin arzikin dijital da ayyukan masu kare muhalli da sufurin sama da hidimomin kudi da cinikayya ta yanar gizo da sauransu.

 

Bugu da kari, rahoton ya ce ta hanyar zuba jari dake mayar da hankali ga harkokin kasuwanci, jarin Sin kan ababen more rayuwa da sauran sabbin bangarori suna bunkasa tsarin ayyukan masana’atu da ma daukaka darajarsu.

 

Da yake jawabi, tsohon ministan kudi da tsare-tsare na kasar Habasha kuma mai neman digirin-digirgir a cibiyar nazarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa a jami’ar Peking ta kasar Sin Endalkachew Sime, ya bayyana rahoton a matsayin mai muhimmanci wajen tsara dabaru da manufofi, saboda yadda ya yi bayani dalla-dalla kan bangarorin hadin gwiwa da wadanda ya kamata a mayar da hankali kan su, da ma kalubalen da ake fuskanta. Haka kuma zai kara aminci tsakanin bangarorin biyu da kyautata muhallin hadin gwiwa.

 

Shi kuwa masanin tattalin arziki kuma tsohon ma’aikacin bankin duniya kuma mashawarcin shugaban kasar Kenya kan harkokin tattalin arziki, Dr. Mwangi Wachira, cewa ya yi, yayin da kasashen nahiyar Afrika ke kokarin neman ci gaba, kasar Sin ta tallafawa wannan kokari ta hanyar gudanar da ayyukan da suka taimaka wajen magance tushen manyan kalubalen nahiyar.

 

Ya ce ana samun nasarar hadin gwiwar bangarorin biyu ne saboda manufofin Sin a bayyane suke, kuma tana taimakawa ba tare da kakaba akidunta kan su ba, wato tana taimakawa wajen zamanantar da Afrika, ta hanyar da ta dace da Afrika.

 

Rahoton ya ce za a kara karfafawa kamfanonin Sin gwiwar zubawa da fada jarinsu a kasashen Afrika, tare da kira ga gwamnatocin nahiyar Afrika su kyautata muhallin kasuwanci da inganta dangantakar Sin da Afrika. (Fa’iza Mustapha)

 

 

Afrika
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Afrika
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Sulaiman
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Sulaiman
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

MASU ALAKA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
Daga Birnin Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
Daga Birnin Sin

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Next Post
Yadda Ake Miyar Tafasa Ta Gargajiya

Yadda Ake Miyar Tafasa Ta Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran

June 21, 2026
‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.