ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Karfafawa Karin Kamfanonin Kasar Sin Gwiwar Zuba Jari A Nahiyar Afrika

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afrika

Cibiyar bunkasa zuba jari a nahiyar Afrika ta kasar Sin (CABC), ta kaddamar da rahoto kan jarin da kamfanonin kasar Sin suka zuba a nahiyar Afrika na 2024. 

 

Rahoton wanda aka kaddamar da yammacin jiya Juma’a, ya bayyana nasarorin da aka samu da sabbin bangarori da ma damarmakin zuba jari dake akwai a kasashen Afrika.

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar
  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Sadarwa

A kan fitar da rahoton a kowacce shekara tun daga shekarar 2021. Wannan sakamako ne na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika FOCAC, karkashin jadawalin aikin da ake son gudanarwa daga 2021-2024, wanda aka fitar a Dakar na kasar Senegal. Kuma a bana, rahoton na zuwa ne gabanin taron na FOCAC wanda za a yi a Beijing, daga ranar 4 zuwa 6 ga watan Satumba mai zuwa.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

A jawabinsa na bude taron, babban shugaban majalisar CABC, Wang Xiaoyong ya bayyana dandalin FOCAC a matsayin wata kadara mai daraja ga Sin da Afirka.

 

Yana mai cewa, sun yi ammana cikin shekaru 3 masu zuwa, karkashin dabaru daga gwamnatocin Sin da Afirka, da goyon baya daga bangarorin diplomasiyya da cinikayya da hada-hadar kudi, hadin gwiwar Sin da Afrika a bangarorin tattalin arziki da cinikayya da zuba jari, zai kai ga zamanantar da nahiyar Afrika.

 

A cewar rahoton, zuwa karshen shekarar 2022, jarin da Sin ta zuba kai tsaye a nahiyar Afrika ya zarce dala biliyan 47, kuma sama da kamfanonin Sin 3,000 ne suka zuba jari tare da gudanar da harkokin kasuwanci a Afrika. kana a rabin farko na shekarar 2023, jarin kai tsaye na Sin a Afrika ya zarce dala biliyan 1.82, wanda ya karu da kaso 4.4 a kowacce shekara.

 

Rahoton ya kara da cewa, kasar Sin na kara yawan jarinta a Afrika a bangarori daban daban, inda ta kara fadadawa zuwa bangarorin masu tasowa kamar na tattalin arzikin dijital da ayyukan masu kare muhalli da sufurin sama da hidimomin kudi da cinikayya ta yanar gizo da sauransu.

 

Bugu da kari, rahoton ya ce ta hanyar zuba jari dake mayar da hankali ga harkokin kasuwanci, jarin Sin kan ababen more rayuwa da sauran sabbin bangarori suna bunkasa tsarin ayyukan masana’atu da ma daukaka darajarsu.

 

Da yake jawabi, tsohon ministan kudi da tsare-tsare na kasar Habasha kuma mai neman digirin-digirgir a cibiyar nazarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa a jami’ar Peking ta kasar Sin Endalkachew Sime, ya bayyana rahoton a matsayin mai muhimmanci wajen tsara dabaru da manufofi, saboda yadda ya yi bayani dalla-dalla kan bangarorin hadin gwiwa da wadanda ya kamata a mayar da hankali kan su, da ma kalubalen da ake fuskanta. Haka kuma zai kara aminci tsakanin bangarorin biyu da kyautata muhallin hadin gwiwa.

 

Shi kuwa masanin tattalin arziki kuma tsohon ma’aikacin bankin duniya kuma mashawarcin shugaban kasar Kenya kan harkokin tattalin arziki, Dr. Mwangi Wachira, cewa ya yi, yayin da kasashen nahiyar Afrika ke kokarin neman ci gaba, kasar Sin ta tallafawa wannan kokari ta hanyar gudanar da ayyukan da suka taimaka wajen magance tushen manyan kalubalen nahiyar.

 

Ya ce ana samun nasarar hadin gwiwar bangarorin biyu ne saboda manufofin Sin a bayyane suke, kuma tana taimakawa ba tare da kakaba akidunta kan su ba, wato tana taimakawa wajen zamanantar da Afrika, ta hanyar da ta dace da Afrika.

 

Rahoton ya ce za a kara karfafawa kamfanonin Sin gwiwar zubawa da fada jarinsu a kasashen Afrika, tare da kira ga gwamnatocin nahiyar Afrika su kyautata muhallin kasuwanci da inganta dangantakar Sin da Afrika. (Fa’iza Mustapha)

 

 

Afrika
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Afrika
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Yadda Ake Miyar Tafasa Ta Gargajiya

Yadda Ake Miyar Tafasa Ta Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.