Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya yi kira ga al’ummun kasa da kasa da su dunkule waje guda, kuma su himmatu matuka wajen gudanar da ayyukan jin kai.
Sun, wanda ya yi kiran a jiya Juma’a, yayin babban taron mahawarar shekarar nan ta 2026 dangane da ayyukan jin kai, wadda ta gudana karkashin majalisar tattalin arziki da zamantakewa ta MDD, ya ce yanzu haka yanayin jin kai a sassa daban daban na duniya ya tsananta. Ayyukan masu dauke da makamai sun haifar da tarin asarar rayuka da raba al’ummu da muhallansu, yayin da kuma sauyin yanayi, da bala’u daga indallahi ke kara ta’azzara halin matsin rayuwa da jama’a ke fama da shi.
Sun Lei, ya kara da cewa, gibin kudaden tallafi da ake bukata na kara fadada. Don haka kasar Sin ke kira ga masu bayar da tallafi, da su cika alkawuran da suka dauka bisa gaskiya, tare da kara azamar sauke nauyin tallafin dake wuyansu.
Ya ce, ya kamata a daidaita samar da gudunmawa. Fatan shi ne MDD za ta daidaita mika dan abun da yake hannunta ga mabukata, da mayar da hankali wajen tallafawa wuraren dake cikin matsanancin yanayin jin kai, masu fama da kamfar kudade, da tsayin lokaci cikin bukatuwar agaji.
Jami’in na kasar Sin ya ce, karancin ci gaba na daya daga cikin ginshikan dake haifar da fadawa cikin yanayin jin kai. Don haka ya kamata sassan kasa da kasa su hade bukatun kasashen da ake tallafawa, tare da mayar da hankali ga tsare-tsaren tallafin jin kai da tallafin samar da ci gaba, da kyautata ikon bunkasa kasashen dake cikin bukatun jin kai. (Saminu Alhassan)














