ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

by Sulaiman
2 days ago

A yayin da al’ummar Musulmi a faɗin duniya ke shiga sabuwar shekarar Musulunci (Muharram, 1448H) a ranar Talata, Ƙungiyar Malaman Addinin Musulunci, reshen Jihar Ogun, ta yi kira ga mabiya addinin Musulunci a faɗin ƙasar nan da su sadaukar da rayuwarsu, wajen tabbatar da adalci, riƙon amana, mutunta Ɗan’adam da sauran kyawawan ɗabi’un da ake buƙata cikin gaggawa, domin samar da zaman lafiya a duniya.

Dangane da zaman lafiya, haɗin kai da haƙuri da wahalhalu, ƙungiyar ta ce; ya kamata Musulmin Nijeriya, su yi nazari kan al’amuran zamantakewa da siyasa na wannan lokaci, “yayin da ɗaiɗaikun mutane da al’ummomi ke fuskantar ƙalubale da dama”.

Da yake jawabi a taron manema labarai na duniya a ranar Talata a Abeokuta, babban birnin jihar, Shugaban PMC, Alhaji Abdul Wasiu Akinyemi, ya ce; ƙa’idojin Hijira na nan daram a yau. Don haka, masu bin addinin Musulunci na buƙatar su yi tunani a kan darussan da za su bayar, su ba da tasu gudummawar wajen gina al’ummar Nijeriya “mafi zaman lafiya, daidaito da kuma wadata”.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa, Hijrah wata dabara ce ta ruhi da zamantakewa da siyasa, wacce ta kafa tushen samar da al’umma mai adalci da wadata, Akinyemi ya yi kira ga masu bin addinin Musulunci da su tabbatar da cewa, suna gudanar da adalci da riƙon amana da kuma mutunta Ɗan’adam kowa da kowa a Nijeriya, yana mai jaddada cewa; “babu wata al’umma da za ta ci gaba, ba tare da kwatanta gaskiya da adalci ba”.

“A matsayinmu na ƴan ƙasa kuma shugabanni, dole ne mu bayar da shawarar tabbatar da gaskiya a cikin shugabanci, riƙe amana a ofisoshin gwamnati, kare haƙƙin bil’adama, rarraba albarkatun ƙasa, bin doka da oda da kuma aiwatar da adalci a zamantakewa. Babu wata al’umma da za ta ci gaba, ba tare da kwatanta gaskiya da adalci a tsakaninta ba”.

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

“A cikin al’ummominmu daban-daban, ya kamata musulmi da gangan su inganta tattaunawa tsakanin addinai, zaman lafiya, mutunta bambance-bambancen al’adu, haɗin kan ƙasa da zamantakewar al’umma.

Rarrabuwa tana raunana al’umma, yayin da haɗin kai yake ƙarfafa su”.

Shugaban na PMC ya kuma yi kira da a ƙara saka jari a fannin ilimi mai inganci, koyon sana’o’i, kasuwanci, hada-hadar jama’a, da kuma inganta tarbiyyar matasan Nijeriya, bisa la’akari da muhimmancin yawan jama’arsu da kuma ɗimbin ƙarfin da suke da shi.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

MASU ALAKA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato
Manyan Labarai

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus
Labarai

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Next Post
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.