ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

by Sulaiman
3 weeks ago

A yayin da al’ummar Musulmi a faɗin duniya ke shiga sabuwar shekarar Musulunci (Muharram, 1448H) a ranar Talata, Ƙungiyar Malaman Addinin Musulunci, reshen Jihar Ogun, ta yi kira ga mabiya addinin Musulunci a faɗin ƙasar nan da su sadaukar da rayuwarsu, wajen tabbatar da adalci, riƙon amana, mutunta Ɗan’adam da sauran kyawawan ɗabi’un da ake buƙata cikin gaggawa, domin samar da zaman lafiya a duniya.

Dangane da zaman lafiya, haɗin kai da haƙuri da wahalhalu, ƙungiyar ta ce; ya kamata Musulmin Nijeriya, su yi nazari kan al’amuran zamantakewa da siyasa na wannan lokaci, “yayin da ɗaiɗaikun mutane da al’ummomi ke fuskantar ƙalubale da dama”.

Da yake jawabi a taron manema labarai na duniya a ranar Talata a Abeokuta, babban birnin jihar, Shugaban PMC, Alhaji Abdul Wasiu Akinyemi, ya ce; ƙa’idojin Hijira na nan daram a yau. Don haka, masu bin addinin Musulunci na buƙatar su yi tunani a kan darussan da za su bayar, su ba da tasu gudummawar wajen gina al’ummar Nijeriya “mafi zaman lafiya, daidaito da kuma wadata”.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa, Hijrah wata dabara ce ta ruhi da zamantakewa da siyasa, wacce ta kafa tushen samar da al’umma mai adalci da wadata, Akinyemi ya yi kira ga masu bin addinin Musulunci da su tabbatar da cewa, suna gudanar da adalci da riƙon amana da kuma mutunta Ɗan’adam kowa da kowa a Nijeriya, yana mai jaddada cewa; “babu wata al’umma da za ta ci gaba, ba tare da kwatanta gaskiya da adalci ba”.

“A matsayinmu na ƴan ƙasa kuma shugabanni, dole ne mu bayar da shawarar tabbatar da gaskiya a cikin shugabanci, riƙe amana a ofisoshin gwamnati, kare haƙƙin bil’adama, rarraba albarkatun ƙasa, bin doka da oda da kuma aiwatar da adalci a zamantakewa. Babu wata al’umma da za ta ci gaba, ba tare da kwatanta gaskiya da adalci a tsakaninta ba”.

LABARAI MASU NASABA

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

“A cikin al’ummominmu daban-daban, ya kamata musulmi da gangan su inganta tattaunawa tsakanin addinai, zaman lafiya, mutunta bambance-bambancen al’adu, haɗin kan ƙasa da zamantakewar al’umma.

Rarrabuwa tana raunana al’umma, yayin da haɗin kai yake ƙarfafa su”.

Shugaban na PMC ya kuma yi kira da a ƙara saka jari a fannin ilimi mai inganci, koyon sana’o’i, kasuwanci, hada-hadar jama’a, da kuma inganta tarbiyyar matasan Nijeriya, bisa la’akari da muhimmancin yawan jama’arsu da kuma ɗimbin ƙarfin da suke da shi.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • Sulaiman
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

MASU ALAKA

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
Labarai

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Labarai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
Next Post
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.