A yayin da al’ummar Musulmi a faɗin duniya ke shiga sabuwar shekarar Musulunci (Muharram, 1448H) a ranar Talata, Ƙungiyar Malaman Addinin Musulunci, reshen Jihar Ogun, ta yi kira ga mabiya addinin Musulunci a faɗin ƙasar nan da su sadaukar da rayuwarsu, wajen tabbatar da adalci, riƙon amana, mutunta Ɗan’adam da sauran kyawawan ɗabi’un da ake buƙata cikin gaggawa, domin samar da zaman lafiya a duniya.
Dangane da zaman lafiya, haɗin kai da haƙuri da wahalhalu, ƙungiyar ta ce; ya kamata Musulmin Nijeriya, su yi nazari kan al’amuran zamantakewa da siyasa na wannan lokaci, “yayin da ɗaiɗaikun mutane da al’ummomi ke fuskantar ƙalubale da dama”.
Da yake jawabi a taron manema labarai na duniya a ranar Talata a Abeokuta, babban birnin jihar, Shugaban PMC, Alhaji Abdul Wasiu Akinyemi, ya ce; ƙa’idojin Hijira na nan daram a yau. Don haka, masu bin addinin Musulunci na buƙatar su yi tunani a kan darussan da za su bayar, su ba da tasu gudummawar wajen gina al’ummar Nijeriya “mafi zaman lafiya, daidaito da kuma wadata”.
Ya bayyana cewa, Hijrah wata dabara ce ta ruhi da zamantakewa da siyasa, wacce ta kafa tushen samar da al’umma mai adalci da wadata, Akinyemi ya yi kira ga masu bin addinin Musulunci da su tabbatar da cewa, suna gudanar da adalci da riƙon amana da kuma mutunta Ɗan’adam kowa da kowa a Nijeriya, yana mai jaddada cewa; “babu wata al’umma da za ta ci gaba, ba tare da kwatanta gaskiya da adalci ba”.
“A matsayinmu na ƴan ƙasa kuma shugabanni, dole ne mu bayar da shawarar tabbatar da gaskiya a cikin shugabanci, riƙe amana a ofisoshin gwamnati, kare haƙƙin bil’adama, rarraba albarkatun ƙasa, bin doka da oda da kuma aiwatar da adalci a zamantakewa. Babu wata al’umma da za ta ci gaba, ba tare da kwatanta gaskiya da adalci a tsakaninta ba”.
“A cikin al’ummominmu daban-daban, ya kamata musulmi da gangan su inganta tattaunawa tsakanin addinai, zaman lafiya, mutunta bambance-bambancen al’adu, haɗin kan ƙasa da zamantakewar al’umma.
Rarrabuwa tana raunana al’umma, yayin da haɗin kai yake ƙarfafa su”.
Shugaban na PMC ya kuma yi kira da a ƙara saka jari a fannin ilimi mai inganci, koyon sana’o’i, kasuwanci, hada-hadar jama’a, da kuma inganta tarbiyyar matasan Nijeriya, bisa la’akari da muhimmancin yawan jama’arsu da kuma ɗimbin ƙarfin da suke da shi.














Discussion about this post