Shugaban ƙungiyar Kyautal Pulaako Pulbe ta Jihar Nasarawa Alhaji Ibrahim Dare shi ne wanda ya yi wannan kiran ne a ranar Asabar ta makon da ya gabata a makarantar Firamare ta garin Gunki lokacin da aka rantsar Shugabannin ƙungiyar na Ƙaramar Hukumar ta Nasarawan Toto. Bugu da ƙari ya tunatar da su muhimmancin neman shawara daga wurin waɗanda suke shugaban ta, saboda ba komai ba ne za su aiwatar ba tare da tuntubar waɗanda suke jagoranta, ko kuma a tsakanin su ba.
Mutane 30 ne aka rantsar da Shugabannin ƙungiyar Kyautal Pulaako Pulbe ta ƙaramar Hukumar Nasarawaran Toto a ƙarƙashin jagorancin Usman Sodangi wanda shi ne Shugaban ƙungiyar na ƙaramar Hukumar.
Da yake jawabi Shugaban ƙungiyar Kyautal Pulaaku Pulbe na ƙaramara Hukumar Nasarawan Toto Usman Sodangi ya nuna jin daɗin sa danagane da Shugabancin ƙungiyar da aka ba shi, da kuma ɗaukar da lalkawarin zai tafiyar da harkar jagorancin ƙungiyar cikin gaskiya da riƙon amana, haka ne kowane daga cikin sauran Shugabannin ƙungiyar za su yi.
Da yake na shi jawabin Ko’odineta na Jihar Yusuf Abubakar wanda aka fisani da suna Kwamanda hamdala ce ya yi cewa Alhamdu lillahi sun samu babban ci gaba ƙwarai da gaske domin kuwa mutane sun fara gane muhimmancin ƙungiyar, ya kuma yi kira da Ahmed Sodangi da cewa ya yi biyayya ga waɗanda suke gaba da shi a Shugabancin da kuma sa haƙuri a dukkan hulɗoɗin da zai yi da mutane.
Shi ma Ardon Ara Idris Sulaiman bai bari an bar shi a baya ba wajen ba Shugaban ƙungiyar shawara in da ya ce ya san shi mutumin kirki ne ga kuma son gaskiya da riƙon amana amma a wani lokaci abubuwa kan canza ta wajen amfani da shawarwarin da wasu za su bada, da ba na gaskiya ba, sai dai kawai waɗanda kan bada shawarwarin sun son su kai shi zuwa idan ya kai ga shiga ba zai iya fitowa lafiya ba.














Discussion about this post