Sojojin rundunar Operation FANSAN YAMMA, sun ceto mutane 22 a wasu hare-hare guda biyu da aka kai a Jihar Sakkwato.Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato
A cewar rundunar sojin, farmakin farko ya biyo bayan sahihin bayanan da aka samu cewa ‘yan ta’adda sun tare hanyar Sabon Birni zuwa Shinkafi a ƙauyen Kura Mota, inda suka kai hari kan motoci biyu, suka kashe mutum ɗaya tare da sace wasu fasinjoji.
Sojoji sun ƙaddamar da farmaki ta ƙasa da kuma amfani da jirgin sama, wanda ya tilasta wa ‘yan bindigar barin waɗanda suka sace.
An ceto mutane 17 tare da miƙa su ga hukumomin tsaro.
A ranar kuma, sojoji sun daƙile yunƙurin sace manoma a ƙauyen Chohi.
Sojojin sun bi sahun maharan sannan suka ceto manoma biyar, waɗanda aka mayar da su cikin iyalansu.
Bayan wannan aiki, rundunar sojin ta yi sintiri a ƙauyuka kamar Gidan Rana da Gidan Sale domin tabbatar da tsaro da hana sake kai hare-hare a yankin.















Discussion about this post