Sassa daban daban na kasar Kyrgyzstan sun darajanta ziyarar aiki da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai kasar kwanan nan. A ranar 31 ga watan Agusta, shugabannin kasashen biyu sun yi ganawa a birnin Bishkek, fadar mulkin kasar Kyrgyzstan, inda Xi ya bayyana fatan karfafa hadin gwiwar kasashen biyu, domin zurfafa aikin kafa makomarsu ta bai daya.
A nasa bangare kuma, shugaba Sadyr Japarov ya ce, ziyarar shugaba Xi a kasarsa, ta shaida dankon zumunci da kyakkyawar fahimtar juna a siyasance tsakanin kasashen biyu.
A matsayin kasashen dake cikin mambobin da suka kafa kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai (SCO), kuma kasashe masu tasowa, kasar Sin da kasar Kyrgyzstan suna da matsayi kusan iri daya a fannin kiyaye adalci wajen daidaita harkokin kasashen duniya, da kara bude kofa da hakuri da juna don neman samu ci gaba, lamarin da ya nuna muhimmiyar ma’anar kafa makomar Sin da Kyrgyzstan ta bai daya. Ya kamata a aiwatar da ra’ayi bai daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma bisa manufar sada zumunci da neman wadata tare, ta yadda za su bayar da karin gudummawa a fannonin shimfida zaman lafiya, da tabbatar da zaman karko, da samun wadata a yankin da ma kasashen duniya baki daya. (Mai Fassara: Maryam Yang)














