• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabin Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu Mataki Ne Mafi Cancanta- In ji Zulum

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Siyasa
0
Zabin Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu Mataki Ne Mafi Cancanta- In ji Zulum
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana zabo Sanata Kashim Shettima a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC wanda Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin hangen nesa kuma mataki mafi dacewa da cancanta. 

Zulum ya bayyana hakan a wata sanarwar manema labaru wadda ya sanya wa hannu kuma aka raba wa ‘yan jaridu, da yammacin ranar Lahadi a birnin Maiduguri.

  • Goron Sallah: Shugaban APC Ya Yi Wa Nijeriya Addu’ar Zaman Lafiya
  • Buhari Zai Inganta Harkokin Tsaro Kafin Karshen Wa’adin Mulkinsa —Malami

“Yau na yi matukar farin ciki dangane da muhimmin labarin sanarwar da ta riskeni cewa shugabana abin koyi, inda dan takarar shugaban kasarmu a jam’iyyar APC a zaben 2023 mai zuwa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya zabi Sanata Kashim Shettima matsayin mataimakinsa. Wanda ko shakka babu wannan shi ne babban burin da nake da shi na ganin Sanata Kashim Shettima ya samu wannan dama wadda ya cancanta kuma ya dace, a matsayin daya daga cikin shugabani masu kishin Nijeriya a zukatansu.”

“A wajena, kuma ina da tabbacin kaso mai yawa a cikin shugabanni da ‘yan jam’iyyar APC, sun yi na’am da wannan hangen nesa wanda Tinubu ya yi na zabo Sanata Kashim Shettima a daidai wannan lokaci na bukatar hakan.”

“Zabar Shettima al’amari ne wanda ya shafeni a kashin kaina, tare da shugabaninmu hadi da baki dayan masu ruwa da tsaki da mambobin jam’iyyar APC, wanda nake da tabbacin cewa zamu tashi tsaye haikan, mu yi aiki tukuru, babu dare ba rana wajen yakin neman zabe domin samun gagarumar nasara a zaben 2023, in Sha Allah.”

Labarai Masu Nasaba

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

“Bugu da kari, ko shakka babu, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi dacen zaben shugaba nagari, ya zabi mutumin da ya san Nijeriya ciki da bayanta tare da kalubalen da take fuskanta. Wanda a cikin kabilun da suke jihohin Nijeriya 36 hadi da Abuja, babu wanda Sanata Kashim Shettima ba zai gaza yin gamsasshen bayani a kansa ba. Saboda yadda yake da masaniya kan yanayin mu’amalarsu ta rayuwa, al’adu, addini, tsarin tattalin arziki, da tsarin siyasarsu- a dukan wadannan jihohi 36 hadi da Abuja.”

“Shettima hakikanin dan kishin kasa ne, wanda ya yi imani kan hadin kan kasa, tare da tabbatar da hakan a wurare daban-daban a rayuwarsa.”

“A hannu guda kuma, abu mafi muhimmancin dai shi ne, Tinubu ya yi zaba wa Nijeriya mataimakin shugaban kasa mai zuwa, in sha Allah, wanda kuma hakan mataki ne na hangen nesa tare da amfani da ilimi kuma a cikin cancanta, kuma hakan zai habaka ci gaban tattalin arzikin Nijeriya, duniya ma sai ta shaidi hakan.”

“Ina da abubuwan fada masu yawan gaske dangane da Sanata Kashim Shettima, amma na takaice su har sai lokacin yakin neman zabe.”

“A hannu guda kuma, zan yi amfani da wannan dama wajen bayyana jinjina da girmamawa ga shugaban jam’iyyar mu, shugaban kasa Muhammadu Buhari, bisa kyakkyawan shugabancin da ya gudanar a cikin wadannan shekaru tare da cikakken goyon bayan zaben Sanata Shettima ya marawa dan takarar shugaban kasa.”

“Har wala yau kuma muna yaba wa shugabanin majalisar zartaswa na kasa a jam’iyyar APC tare da mambobin kwamitin kwararru da dattawanmu na jam’iyyar hadi da ilahirin masu ruwa da tsaki a gudanar da jam’iyyar APC.”

“Muna yaba wa jajircewar baki xayan Gwamnonin APC a kararshin jagorancin babban yayana, Gwamnan jihar Kebbi, Sanata Atiku Bagudu.”

“Haka zalika da dukan shugabanin jam’iyyar APC da masu ruwa da tsaki a Arewa Maso Gabas bisa cikakken goyon bayansu, shugabanin jam’iyyar APC a jihar Borno da dimbin magoya baya, muna matukar godiya.” Gwamna Zulum.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCSanataShettimatakaraTinubuZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 18 A Zamfara, Mutane Sun Tsere Daga Gidajensu

Related

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
Da ɗumi-ɗuminsa

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

7 hours ago
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum
Da ɗumi-ɗuminsa

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

8 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

9 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

1 day ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

1 day ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

2 days ago
Next Post
Shettima

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 18 A Zamfara, Mutane Sun Tsere Daga Gidajensu

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.