• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabin Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu Mataki Ne Mafi Cancanta- In ji Zulum

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Siyasa
0
Zabin Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu Mataki Ne Mafi Cancanta- In ji Zulum
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana zabo Sanata Kashim Shettima a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC wanda Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin hangen nesa kuma mataki mafi dacewa da cancanta. 

Zulum ya bayyana hakan a wata sanarwar manema labaru wadda ya sanya wa hannu kuma aka raba wa ‘yan jaridu, da yammacin ranar Lahadi a birnin Maiduguri.

  • Goron Sallah: Shugaban APC Ya Yi Wa Nijeriya Addu’ar Zaman Lafiya
  • Buhari Zai Inganta Harkokin Tsaro Kafin Karshen Wa’adin Mulkinsa —Malami

“Yau na yi matukar farin ciki dangane da muhimmin labarin sanarwar da ta riskeni cewa shugabana abin koyi, inda dan takarar shugaban kasarmu a jam’iyyar APC a zaben 2023 mai zuwa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya zabi Sanata Kashim Shettima matsayin mataimakinsa. Wanda ko shakka babu wannan shi ne babban burin da nake da shi na ganin Sanata Kashim Shettima ya samu wannan dama wadda ya cancanta kuma ya dace, a matsayin daya daga cikin shugabani masu kishin Nijeriya a zukatansu.”

“A wajena, kuma ina da tabbacin kaso mai yawa a cikin shugabanni da ‘yan jam’iyyar APC, sun yi na’am da wannan hangen nesa wanda Tinubu ya yi na zabo Sanata Kashim Shettima a daidai wannan lokaci na bukatar hakan.”

“Zabar Shettima al’amari ne wanda ya shafeni a kashin kaina, tare da shugabaninmu hadi da baki dayan masu ruwa da tsaki da mambobin jam’iyyar APC, wanda nake da tabbacin cewa zamu tashi tsaye haikan, mu yi aiki tukuru, babu dare ba rana wajen yakin neman zabe domin samun gagarumar nasara a zaben 2023, in Sha Allah.”

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

“Bugu da kari, ko shakka babu, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi dacen zaben shugaba nagari, ya zabi mutumin da ya san Nijeriya ciki da bayanta tare da kalubalen da take fuskanta. Wanda a cikin kabilun da suke jihohin Nijeriya 36 hadi da Abuja, babu wanda Sanata Kashim Shettima ba zai gaza yin gamsasshen bayani a kansa ba. Saboda yadda yake da masaniya kan yanayin mu’amalarsu ta rayuwa, al’adu, addini, tsarin tattalin arziki, da tsarin siyasarsu- a dukan wadannan jihohi 36 hadi da Abuja.”

“Shettima hakikanin dan kishin kasa ne, wanda ya yi imani kan hadin kan kasa, tare da tabbatar da hakan a wurare daban-daban a rayuwarsa.”

“A hannu guda kuma, abu mafi muhimmancin dai shi ne, Tinubu ya yi zaba wa Nijeriya mataimakin shugaban kasa mai zuwa, in sha Allah, wanda kuma hakan mataki ne na hangen nesa tare da amfani da ilimi kuma a cikin cancanta, kuma hakan zai habaka ci gaban tattalin arzikin Nijeriya, duniya ma sai ta shaidi hakan.”

“Ina da abubuwan fada masu yawan gaske dangane da Sanata Kashim Shettima, amma na takaice su har sai lokacin yakin neman zabe.”

“A hannu guda kuma, zan yi amfani da wannan dama wajen bayyana jinjina da girmamawa ga shugaban jam’iyyar mu, shugaban kasa Muhammadu Buhari, bisa kyakkyawan shugabancin da ya gudanar a cikin wadannan shekaru tare da cikakken goyon bayan zaben Sanata Shettima ya marawa dan takarar shugaban kasa.”

“Har wala yau kuma muna yaba wa shugabanin majalisar zartaswa na kasa a jam’iyyar APC tare da mambobin kwamitin kwararru da dattawanmu na jam’iyyar hadi da ilahirin masu ruwa da tsaki a gudanar da jam’iyyar APC.”

“Muna yaba wa jajircewar baki xayan Gwamnonin APC a kararshin jagorancin babban yayana, Gwamnan jihar Kebbi, Sanata Atiku Bagudu.”

“Haka zalika da dukan shugabanin jam’iyyar APC da masu ruwa da tsaki a Arewa Maso Gabas bisa cikakken goyon bayansu, shugabanin jam’iyyar APC a jihar Borno da dimbin magoya baya, muna matukar godiya.” Gwamna Zulum.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCSanataShettimatakaraTinubuZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 18 A Zamfara, Mutane Sun Tsere Daga Gidajensu

Related

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

9 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

11 hours ago
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
Da ɗumi-ɗuminsa

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

2 days ago
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum
Da ɗumi-ɗuminsa

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

2 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

2 days ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

2 days ago
Next Post
Shettima

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 18 A Zamfara, Mutane Sun Tsere Daga Gidajensu

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.