ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabin Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu Mataki Ne Mafi Cancanta- In ji Zulum

by Muhammad Maitela
4 years ago
Shettima

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana zabo Sanata Kashim Shettima a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC wanda Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin hangen nesa kuma mataki mafi dacewa da cancanta. 

Zulum ya bayyana hakan a wata sanarwar manema labaru wadda ya sanya wa hannu kuma aka raba wa ‘yan jaridu, da yammacin ranar Lahadi a birnin Maiduguri.

  • Goron Sallah: Shugaban APC Ya Yi Wa Nijeriya Addu’ar Zaman Lafiya
  • Buhari Zai Inganta Harkokin Tsaro Kafin Karshen Wa’adin Mulkinsa —Malami

“Yau na yi matukar farin ciki dangane da muhimmin labarin sanarwar da ta riskeni cewa shugabana abin koyi, inda dan takarar shugaban kasarmu a jam’iyyar APC a zaben 2023 mai zuwa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya zabi Sanata Kashim Shettima matsayin mataimakinsa. Wanda ko shakka babu wannan shi ne babban burin da nake da shi na ganin Sanata Kashim Shettima ya samu wannan dama wadda ya cancanta kuma ya dace, a matsayin daya daga cikin shugabani masu kishin Nijeriya a zukatansu.”

ADVERTISEMENT

“A wajena, kuma ina da tabbacin kaso mai yawa a cikin shugabanni da ‘yan jam’iyyar APC, sun yi na’am da wannan hangen nesa wanda Tinubu ya yi na zabo Sanata Kashim Shettima a daidai wannan lokaci na bukatar hakan.”

“Zabar Shettima al’amari ne wanda ya shafeni a kashin kaina, tare da shugabaninmu hadi da baki dayan masu ruwa da tsaki da mambobin jam’iyyar APC, wanda nake da tabbacin cewa zamu tashi tsaye haikan, mu yi aiki tukuru, babu dare ba rana wajen yakin neman zabe domin samun gagarumar nasara a zaben 2023, in Sha Allah.”

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

“Bugu da kari, ko shakka babu, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi dacen zaben shugaba nagari, ya zabi mutumin da ya san Nijeriya ciki da bayanta tare da kalubalen da take fuskanta. Wanda a cikin kabilun da suke jihohin Nijeriya 36 hadi da Abuja, babu wanda Sanata Kashim Shettima ba zai gaza yin gamsasshen bayani a kansa ba. Saboda yadda yake da masaniya kan yanayin mu’amalarsu ta rayuwa, al’adu, addini, tsarin tattalin arziki, da tsarin siyasarsu- a dukan wadannan jihohi 36 hadi da Abuja.”

“Shettima hakikanin dan kishin kasa ne, wanda ya yi imani kan hadin kan kasa, tare da tabbatar da hakan a wurare daban-daban a rayuwarsa.”

“A hannu guda kuma, abu mafi muhimmancin dai shi ne, Tinubu ya yi zaba wa Nijeriya mataimakin shugaban kasa mai zuwa, in sha Allah, wanda kuma hakan mataki ne na hangen nesa tare da amfani da ilimi kuma a cikin cancanta, kuma hakan zai habaka ci gaban tattalin arzikin Nijeriya, duniya ma sai ta shaidi hakan.”

“Ina da abubuwan fada masu yawan gaske dangane da Sanata Kashim Shettima, amma na takaice su har sai lokacin yakin neman zabe.”

“A hannu guda kuma, zan yi amfani da wannan dama wajen bayyana jinjina da girmamawa ga shugaban jam’iyyar mu, shugaban kasa Muhammadu Buhari, bisa kyakkyawan shugabancin da ya gudanar a cikin wadannan shekaru tare da cikakken goyon bayan zaben Sanata Shettima ya marawa dan takarar shugaban kasa.”

“Har wala yau kuma muna yaba wa shugabanin majalisar zartaswa na kasa a jam’iyyar APC tare da mambobin kwamitin kwararru da dattawanmu na jam’iyyar hadi da ilahirin masu ruwa da tsaki a gudanar da jam’iyyar APC.”

“Muna yaba wa jajircewar baki xayan Gwamnonin APC a kararshin jagorancin babban yayana, Gwamnan jihar Kebbi, Sanata Atiku Bagudu.”

“Haka zalika da dukan shugabanin jam’iyyar APC da masu ruwa da tsaki a Arewa Maso Gabas bisa cikakken goyon bayansu, shugabanin jam’iyyar APC a jihar Borno da dimbin magoya baya, muna matukar godiya.” Gwamna Zulum.

Shettima
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Shettima

'Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 18 A Zamfara, Mutane Sun Tsere Daga Gidajensu

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.