Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin tabbatar da cewa ƙananan hukumomi 774 na Nijeriya suna karɓar kuɗaɗen da aka ware musu kai-tsaye idan ya lashe zaɓen 2027.
Atiku, wanda shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), ya ce zai tabbatar da aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli na shekarar 2024 da ya bai wa ƙananan hukumomi ’yancin amfani da kuɗaɗensu.
Ya ce samun kuɗaɗen kai-tsaye zai taimaka wa ƙananan hukumomi wajen samar da ayyukan more rayuwa, inganta ayyukan jama’a, yaƙi da matsalar tsaro da rage talauci a tsakanin al’umma.
Atiku ya kuma zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da kasa aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli yadda ya kamata.
Ya ce wasu gwamnatocin jihohi na ci gaba da riƙe kuɗaɗen ƙananan hukumomi har yanzu.
Ya ce idan aka zaɓe shi, gwamnatinsa za ta mutunta hukuncin kotu, ta ƙarfafa ’yancin ƙananan hukumomi tare da tabbatar da cewa kuɗin jama’a sun isa inda aka ware su.
Kotun Ƙoli ta yanke hukunci a watan Yulin 2024 cewa ya kamata a riƙa biyan kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai-tsaye daga Asusun Gwamnatin Tarayya.














