ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ZARGIN MAITA: Mahaukaciya Ta Razana Al’umma A Kaduna

by Shehu Yahaya
3 years ago
Kaduna

Al’ummar Unguwar Mangwaron Agwai da Malalin Gabas da ke cikin karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, sun fada cikin rudani kan bayyanar wata mata da suke zargin mayya ce.

Al’ummar wadanda tuni suka fara tserawa suna barin gidajensu domin neman mafaka a unguwanni makwabta.

  • ‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 Tare Da Cafke 9 A Jihar Kaduna.
  • Yadda Bullar Cutar Gansakuka Ta Sa Manoman Citta Tafka Mummunar Asara A Kaduna

lamarin ya faru ne ranar litinin 11 ga watan Satumbar 2023 da misalin karfe 2 na rana, ganin yadda matan suka fito tsirara babu kaya a jikinsu suna yawo layi-layi suna sumbatu lamarin da haifar da tsoro da fargaba a unguwar, musamma mata da matasa.

ADVERTISEMENT

Ganin Hakan ya sanya wasu fusatattu suka kama wata mata mai shekaru kusan 55 suka lakada mata dukan kawo wuka, wacce da kyar jami’an tsaron sai kai na JTF suka kwace ta.

Da farko dai matar ta tsorata kowa hatta jami’an tsaron na JTF sun fara gudu daga ofishin nasu sai daga bisani da suka fahimci cewa matar kamar tana da tabin hankali, hasalima, idan suka bar matasa da matar suna iya daukar doka a hannunsu na yin kisa.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Lokacin da wakilinmu ya shiga unguwar ya yi kicibis da mata da yara suna gudu suna addu’oin neman kariya daga Allah, lamarin da ya kai matan aure suna ta rufe gidanjensu suna barin gida. Wasu mata da wakilinmu ya ci karo da su ya ga suna gudu suna kiran ” mun shiga uku mayu sun shigo mana gari! Ga su can mayu ne su biyu !! .

Binciken da wakilinmu ya gudanar ya nuna cewa matar tana fama da tabin hankali ne ba maita ba, musamman ganin yadda ‘Yan JTF suka rinka yi wa matar tambayoyi.

A zantawarsa da wakilinmu Sakataren JTF na gundumar Mangwaron Agwai Mohammed Suleiman, ya ce “wasu matasa ne suka lakada wa matar duka bisa zargin ita mayya ce saboda sun ganta tana yawo tsirara babu kaya a jikinta hakan ya sanya mu kuma muka kwace ta a hannunsu”

Ya bayyana cewa “Mun fara samun bayanin ne tun da safiyar litinin din nan cewa wasu mata da ake zargin mayu ne sun bayyana a unguwar Mangwaron Agwai sai muka fara bincike a kai zuwa da rana kamar karfe 2, sai muka ga mutane suna ta guje-guje wai mayu sun bayyana a a unguwarmu kamun kace kwabo har wasu fusatattun matasa sun kama wata mata sun lakada mata duka, sun yi mata jina-jina, nan da nan muka kwaci matar domin yi mata tambayoyi da gudanar da bincike akan lamarin”

Ya kara da cewa ” Bayan mun kammala bincikenmu akanta sai muka fahimci cewa matar tana da tabin hankali wanda tuni muka mikata wurin ‘Yansanda a Rafin Guza, inda nan ma suka tabbatar mana da cewa matar tana da tabin hankali kuma zuwa gobe akwai yiwuwar su sake ta” inji shi.

Unguwar Mangwaron Agwai da Malalin Gabas sun yi kaurin suna wajen samun yawaitar mayu da matsalar rashin tsaro, hakan ya sanya matan aure da yara kanana suke zaman dar-dar a yankin.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ postsBio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Manyan Labarai

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
Manyan Labarai

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Next Post
Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

Paul Pogba Na Fuskantar Dakatarwa Bayan Samunsa Da Laifin Shan Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.