ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Sin Da Hannu A Ta’addanci A Nijeriya: Tuggu, Makirci Ne Da Kisisinar Turawan Yamma

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Ta'addanci a Nijeriya

A tsakiyar watan Afrilu ne wata jaridar da ake wallafawa a Birtaniya (The Times) ta yi wani rahoto da ya yi zargin ‘wai’ wasu Sinawa da ke aiki a Nijeriya musamman bangaren ma’adanai suna daukar nauyin ta’addanci a wasu sassa na Nijeriya domin kawai su fake da guzuma su harbi karsana.

Tun daga lokacin da jaridar ta fitar da rahoton ana ci gaba da samun martanoni daban-daban daga masharhanta masu adalci wadanda suke rabe tsaki da tsakuwa. Shi ma ofishin jakadancin Sin da ke Nijeriya ya fitar da sanarwar manema labarai a kan karyata zargin mara tushe balle makama.

  • Ter Stegen Ya Kafa Sabon Tarihi A Barcelona

Idan aka bi rahoton jaridar kan lamarin, za a tarar zargin nata ya ta’allaka ne a kan wata shadara guda daya tak, da ke cewa “shugabannin ‘yan ta’adda sun bugi kirjin cewa a yanzu wuyansu ya isa yanka, hatta Sinawan da ke son aiki (hakar ma’adanai) a yankunan da suke dole su biya kudin haya.” Kuma fa wannan din ma an tsinto ne a wani bidiyo da ke gararamba a shafukan sada zumunta.

ADVERTISEMENT

Idan aka ce an ga wani abu a shafukan sada zumunta, (galibi mu a Nijeriya) ba a daukar abin da muhimmanci har sai an tabbatar da shi daga daya daga cikin shafukan sahihan gidajen jaridu ko takwarorinsu na kafafen yada labarai na lantarki. Domin akwai masu shirya bidiyo ko kirkiro da labari da nufin janyo hankulan jama’a a shafinsu (traffic) saboda taro da sisi da za su iya samu da hakan. A kan wannan, na san da yawa sun yi watsi da rahoton a matsayin zuki ta malle.

Kazalika, ni ban yi mamaki ba da na ji cewa wata jaridar Birtaniya ce ta wallafa rahoton, domin duk mai bibiyar yadda kawancen Sin da Afirka ke bunkasa ci gaba a kasashenmu, ya san da zaman Turawan Yamma ba za su kyale ba, dole za su rika hada tuggu da kisisina da makirce-makircen wargaza lamarin. Domin su sun kasa yin hakan saboda mugunta. Mu dauki misali daga mulkin mallakar da suka yi wa Afirka, tatsar yankin suka yi maimakon kawo masa ci gaba, da yawan masana tarihi sun bayyana cewa da arzikin Afirka ne aka gina Turai. Ta hanyar bautarwa ko cinikin bayi da sace-sacen ma’adanai da suka yi zuwa kasashensu.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

To ma wai, me ya sa Turawan Yamma ba za su yi irin wannan bakin kishin ba, Sin ta samu karbuwa dari bisa dari a Afirka, saboda ta bude wa nahiyar kofofin bunkasa tattalin arziki da samar da ababen more rayuwa. Sin ta gina layukan dogo sama da kilomita 6,000, titunan mota sama da kilomita 6,000, kusan tasoshin teku 20 da kuma manyan tashoshin wutar lantarki sama da 80 a Afirka. Bugu da kari, ta taimaka wajen gina asibitoci da dakunan shan magani sama da 130, da makarantu sama da 170, da filayen wasanni 45 da kuma aiwatar da ayyukan bunkasa noma sama da 500 duk a Afirka.

Yadda mutum zai fahimci alherin da ke cikin wadannan ayyukan shi ne, a Nijeriya, Sin ta gina katafariyar tashar tekun da babu kamarta kaf a Yammacin Afirka a Lekki da ke Jihar Legas. Ana sa rai wannan tashar, ta samar da kudi kusan Dala Biliyan 360 tare da samar da aikin yi akalla Dubu Dari da Saba’in (170,000).

Ke nan me ya sa Turawan Yamma ba za su yi hassada ba, tun da sun riga Sin zuwa nahiyar da shekaru aru-aru amma ba su tsinana komai ba sai bautarwa da sace-sacen dukiyar yankin? Hatta lokacin da suka ce sun bai wa kasashen Afirka ‘yancin cin gashin kai, ba su amince kasashen sun karbi ragamar tafiyar da tattalin arzikinsu ba sai bayan wasu shekaru da suka ga uwar-bari.

Misali mu a Nijeriya, an ba mu ‘yancin kai daga Ingila a 1960, amma ragamar tafiyar da tattalin arzikin kasa bai dawo hannun shugabanninmu baki daya ba sai a 1963.
Abin da Turawan Yamma suka fi kwarewa a kai shi ne kulle-kulle da makirce-makirce a kasashen duniya. Sun fi so su ga ana gwabza yaki a tsakanin ‘yan kasa don wargaza kasa. Misalin abin da ya faru a Libiya ya isa zama shaida, sannan kwanan nan ga gobarar da suka kunna a Sudan.

Ita kuwa Sin, salonta ya bambanta, tana mutunta ‘yancin kasashen da take kawance da su, ta fi yarda da cin gajiyar juna maimakon kashin dankali, ta fi son yaukaka zumunci da inganta zaman lafiya maimakon tashin-tashina. Kokarin da Sin ta yi na sake hade kan Saudiyya da Iran a ‘yan kwanakin baya manuniya ce kan haka.

Tabbas! Lokaci ya yi da Afirka za ta kara nuna wa Turawan Yamma cewa kan mage ya waye, muna bukatar abokan ci gaba ne ba masu kawo koma-baya ba, masu mutunta ‘yancinmu ba masu tilasta mana auren jinsi da keta mana kyawawan al’adu da muka gada ba.

 

Ta'addanci a Nijeriya
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Mene Ne Hukuncin Hada Sittu Shawwal Da Ramuwar Ramadan?

Mene Ne Hukuncin Hada Sittu Shawwal Da Ramuwar Ramadan?

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.