Zhao Leji, shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ya gudanar da ziyarar aiki a kasar Rasha daga ranar 27 zuwa ranar 30 ga watan jiya, bisa gayyatar da Valentina Matviyenko, shugabar majalisar tarayyar kasar, da Vyacheslav Viktorovich Volodin, shugaban majalisar Duma ta kasar suka yi masa.
Inda ya yi shawarwari tare da Matviyenko da Volodin bi da bi, kana ya halarci taro karo na 11 na kwamitin hadin kan majalisun kafa dokoki na kasashen Sin da Rasha.
A yayin taron da aka yi a ranar 28 ga watan jiya, Zhao Le ji ya nuna cewa, ya kamata majalisun kafa dokoki na kasashen biyu su mai da hankali kan muhimman ra’ayoyin bai daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da yarjejeniyoyin hadin kai da bangarorin biyu suka daddale, da kuma muhimman ayyukan da kasashen biyu suka tabbatar, ta yadda za a samu sakamako na a zo a gani. (Kande Gao)















Discussion about this post