Rundunar ‘yansandan jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar mutum biyu tare da sace mutum 30 bayan wani harin ‘yan bindiga da aka kai garin Ayegunle Bunu da ke ƙaramar hukumar Kabba-Bunu a safiyar Litinin.
Rahotanni sun ce maharan sun kai harin ne da misalin ƙarfe 2:25 na dare, inda suka kutsa cikin al’umma tare da tare wata motar haya da ke wucewa yankin. Daga cikin waɗanda aka sace akwai maza 26 da mata huɗu, yayin da wasu daga cikin mutanen ƙauyen ma suka faɗa hannun maharan.
Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan jihar, ASP Afusat Oyiza Saliu, ta ce waɗanda suka rasa rayukansu sun haɗa da Abdullahi Hashimu mai shekaru 22 daga ƙaramar hukumar Igabi ta jihar Kaduna da kuma Cif James Obayomi mai shekaru 65, ɗaya daga cikin mazauna yankin da aka yi garkuwa da su.
Ta ce jami’an tsaro sun fara aikin ceto waɗanda aka sace tare da farautar maharan. Harin ya sake ƙara nuna damuwar da ake yi kan matsalar rashin tsaro a manyan hanyoyi da ƙauyukan jihar Kogi.















Discussion about this post