ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Farmaki Jami’an INEC Tare Da Sace Kayayyakin Zaɓe A Jihar Osun

by Sulaiman
1 month ago
Inec

Rundunar Ƴansandan Jihar Osun ta ƙaddamar da bincike kan zargin kai hari ga jami’an Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) a Ƙaramar Hukumar Odo-Otin, inda wasu da ake zargin ƴan daba ne suka kwashe katunan zaɓe na dindindin (PVCs).

Mai magana da yawun rundunar, DSP Abiodun Ojelabi, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa wasu jami’an INEC da ke rarraba katunan zaɓe na dindindin (PVCs) a Makarantar Firamare ta Oyinlola DC, Ward 2, Ƙaramar Hukumar Odo-Otin, wasu ƴan daba ɗauke da makamai kimanin goma sun kai musu hari.

Ya ce: “An ruwaito cewa ƴan dabar sun yi ta harbe-harbe sama ba ƙaƙƙautawa tare da kwashe fakitin PVC guda uku.”Ojelabi ya ce Kwamishinan Ƴansandan jihar, Ibrahim Gotan, ya yi Allah-wadai da lamarin tare da bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike domin ganowa, kamawa da gurfanar da waɗanda suka aikata laifin.

ADVERTISEMENT

Mai magana da yawun rundunar ya buƙaci jama’a da su kwantar da hankula, su kasance masu bin doka, sannan su guji duk wani mataki da zai iya ƙara haddasa rashin zaman lafiya.

Ojelabi ya kuma roƙi mazauna yankin da waɗanda suka ga abin da ya faru kuma suke da sahihan bayanai da za su taimaka wajen binciken da ake gudanarwa, da su kai rahoto cikin gaggawa zuwa ofishin ƴansanda mafi kusa ko kuma su tuntuɓi rundunar ta lambobin gaggawa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Adedayo Oketola, babban sakataren yaɗa labarai (CPS) na shugaban INEC, Joash Amupitan, ya shaida wa TheCable cewa binciken farko ya nuna cewa an sace wasu na’urorin Bimodal Ɓoter Accreditation System (BVAS) yayin lamarin.

Oketola ya ce: “Ƴansanda sun riga sun fara bincike kan wannan batu, don haka muna jiran sakamakon binciken. Ina ganin sun fara farautar waɗannan mutanen, kuma tabbas sun yi alƙawarin kama su.”Oketola ya ƙara da cewa satar kayayyakin ba za ta kawo cikas ko lalata tsarin zaɓen ba.Za a gudanar da zaɓen Gwamnan Jihar Osun a ranar 15 ga Agusta, 2026.

Inec
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Inec

Kotu Ta Yanke Wa Amaryar Da Ta Kashe Mijinta Kwana Tara Da Aure Hukuncin Kisa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.