Wata Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke wa wata matashiya ‘yar shekara 19 mai suna Saudat Jibrin hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan da ta ‘yanka mijinta mai suna Salisu Idris ɗan shekara 30, kwanaki tara kacal bayan aurensu.
Alkaliyar kotun, Mai Shari’a Maryam Sabo, ta yanke hukuncin ne a ranar Alhamis bayan ta gamsu da hujjojin da masu ƙara suka gabatar. Ta bayyana cewa wadda ake tuhumar tana da kwanaki 90 na daukaka ƙara idan ba ta gamsu ba.
Lauyan mai ƙara, Lamido Abba-Sorondinki, ya shaida wa kotu cewa Saudat ta aikata laifin ne a ranar 5 ga Mayu, 2025, a unguwar Farawa da ke jihar Kano. Ya ce ta zuba guba a cikin zobon mijinta sannan ta yanka masa wuya da wuka da misalin ƙarfe 9 na dare, kwanaki tara bayan bikin su.
A nata ɓangaren, lauyan da ke kare wanda ake tuhumar, Abdulfatah Muhammad, ya nemi kotu da ta yi mata sassauci. Ya bayyana cewa ta tuba yayin da take tsare ta hanyar sauke Alkur’ani Mai Girma, tare da roƙon a duba cewa ita ce ‘ya ta fari da kannanta ke dogaro da ita.














