• Kwamitin Majalisar Dattawa ya bai wa Ojulari wa’adin ranar 13 ga Mayu
Tsohon Babban Daraktan Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL), Mele Kyari, ya bayyana shirinsa na bayar da shaida a binciken da Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ke yi kan zargin bacewar Naira tiriliyan 210 daga asusun kamfanin.
Kwamitin, wanda Sanata Aliyu Wadada ke jagoranta, na binciken rahotannin tantance kuɗaɗen kamfanin mai na shekarun 2017 zuwa 2023.
Kwamitin ya ce har yanzu bai samu gamsassun bayanai daga mahukuntan NNPCL ba kan abin da ya faru da Naira tiriliyan 210 ɗin.Kwamitin Wadada ya sha gayyatar shugaban kamfanin na yanzu, Bayo Ojulari, tare da yin barazanar bayar da umarnin kama shi in yaki amsa gayyatarsu, amma hakan bai haifar da sakamako ba.
Makonni biyu da suka gabata, kwamitin ya sake gayyatar Ojulari tare da umarnin ya zo da Kyari da wasu tsoffin manyan jami’ai biyu — Babban Jami’in Kuɗi, Umar Ajia, da Babban Jami’in Zuba Jari na kayayyakin mai da aka kammala sarrafawa (Upstream), Bala Wunti — zuwa zaman kwamitin na ranar Laraba.
Yayin da Ojulari bai halarta ba a ranar Laraba, Ajia ya halarci zaman inda ya rantse cewa zai bayar da shaida a zama na gaba.
Shi kuwa Kyari, duk da cewa bai halarci zaman ba, amma ya tuntubi Wadada yayin zaman domin tabbatar da cewa shi ma zai bayar da shaida a zama na gaba.
Wani mamba na kwamitin, Sanata Abdul Ningi, shima ya shaida wa takwarorinsa cewa, Wunti ya kira shi yana neman a ƙara masa lokaci domin ya samu damar amsa gayyatar a zama na gaba.
Sanatocin sun nuna rashin jin daɗinsu kan yadda Ojulari ke ci gaba da bayar da uzuri kan rashin halartar zaman kwamitin.
A ƙarshe, kwamitin ya bai wa Ojulari wa’adin zuwa ranar 13 ga Mayu domin ya bayyana gaban kwamitin ko kuma ya fuskanci yiwuwar kama shi bisa umarnin Majalisar Dattawa.















Discussion about this post