ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɓatan Dabon Naira Tiriliyan 210 A NNPCL: Kyari, Ajia da Wunti Sun Shirya Bayar Da Shaida

by Sulaiman
1 month ago
NNPCL

• Kwamitin Majalisar Dattawa ya bai wa Ojulari wa’adin ranar 13 ga Mayu

Tsohon Babban Daraktan Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL), Mele Kyari, ya bayyana shirinsa na bayar da shaida a binciken da Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ke yi kan zargin bacewar Naira tiriliyan 210 daga asusun kamfanin.

Kwamitin, wanda Sanata Aliyu Wadada ke jagoranta, na binciken rahotannin tantance kuɗaɗen kamfanin mai na shekarun 2017 zuwa 2023.

ADVERTISEMENT

Kwamitin ya ce har yanzu bai samu gamsassun bayanai daga mahukuntan NNPCL ba kan abin da ya faru da Naira tiriliyan 210 ɗin.Kwamitin Wadada ya sha gayyatar shugaban kamfanin na yanzu, Bayo Ojulari, tare da yin barazanar bayar da umarnin kama shi in yaki amsa gayyatarsu, amma hakan bai haifar da sakamako ba.

Makonni biyu da suka gabata, kwamitin ya sake gayyatar Ojulari tare da umarnin ya zo da Kyari da wasu tsoffin manyan jami’ai biyu — Babban Jami’in Kuɗi, Umar Ajia, da Babban Jami’in Zuba Jari na kayayyakin mai da aka kammala sarrafawa (Upstream), Bala Wunti — zuwa zaman kwamitin na ranar Laraba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Yayin da Ojulari bai halarta ba a ranar Laraba, Ajia ya halarci zaman inda ya rantse cewa zai bayar da shaida a zama na gaba.

Shi kuwa Kyari, duk da cewa bai halarci zaman ba, amma ya tuntubi Wadada yayin zaman domin tabbatar da cewa shi ma zai bayar da shaida a zama na gaba.

Wani mamba na kwamitin, Sanata Abdul Ningi, shima ya shaida wa takwarorinsa cewa, Wunti ya kira shi yana neman a ƙara masa lokaci domin ya samu damar amsa gayyatar a zama na gaba.

Sanatocin sun nuna rashin jin daɗinsu kan yadda Ojulari ke ci gaba da bayar da uzuri kan rashin halartar zaman kwamitin.

A ƙarshe, kwamitin ya bai wa Ojulari wa’adin zuwa ranar 13 ga Mayu domin ya bayyana gaban kwamitin ko kuma ya fuskanci yiwuwar kama shi bisa umarnin Majalisar Dattawa.

NNPCL
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un
  • Sulaiman
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Sulaiman
    Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?
  • Sulaiman
    A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
Manyan Labarai

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta
Manyan Labarai

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Next Post
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 18 A Yobe

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Tattaunawar Neman Aiki…

June 8, 2026
Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil

June 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance

June 8, 2026
Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.