Iyabo Obasanjo, ƴar tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ta sanar da ficewarta daga jam’iyyar APC, watanni bayan ta kasa samun tikitin takarar gwamnan Jihar Ogun.
A cewar rahoton, Iyabo ta danganta matakin da ta ɗauka da abin da ta bayyana a matsayin rashin mutuntawa da rashin adalci da ta fuskanta a cikin jam’iyyar bayan zaɓen fidda gwani. Ta ce ta yi ƙoƙarin bayar da gudunmawa ga ci gaban jam’iyyar amma ba a ba ta kulawar da ta dace ba.
Tsohuwar Sanatar ta bayyana cewa ficewarta ba ta samo asali daga rashin samun tikiti kaɗai ba, illa ta ce sakamakon yadda aka tafiyar da harkokin jam’iyyar ne da kuma yadda aka mu’amalance ta da ita da magoya bayanta.
Matakin nata na zuwa ne a lokacin da ake ci gaba da samun sauye-sauyen siyasa da sauya sheƙa tsakanin manyan ƴan siyasa gabanin zaɓukan 2027, lamarin da ke ci gaba da sauya fasalin siyasar jihar Ogun da ma ƙasa baki ɗaya.














Discussion about this post