Jam’iyyar ADC ta yi Allah-wadai da hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja wanda ya soke wani hukunci da ya amince da rajistar jam’iyyar NDC, tana mai cewa hakan barazana ce ga dimokuraɗiyyar Nijeriya gabanin babban zaɓen 2026.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran Jam’iyyar na Ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya fitar, ADC ta ce yawaitar amfani da kotuna da matakan gudanarwa kan jam’iyyun adawa na tauye damar dimokuraɗiyya tare da ƙarfafa jam’iyya mai mulki. Ta ce lamarin NDC ba shi kaɗai ba ne, domin wasu jam’iyyun adawa ma sun faɗa cikin rikice-rikicen shari’a.
Jam’iyyar ta jaddada cewa dimokuraɗiyya tana buƙatar adalci, da gasa ta gaskiya da kuma ‘yancin ‘yan ƙasa su zaɓi madadin shugabanci idan bai yi musu ba. Ta kuma yi kira ga ɓangaren shari’a da ya kasance mai zaman kansa, tana gargaɗin cewa bai kamata kotuna su zama kayan cimma manufofin siyasa ba.
ADC ta kuma buƙaci jam’iyyun adawa, da ƙungiyoyin fararen hula, da lauyoyi, da ƙwadago, da kafafen yaɗa labarai da sauran ‘yan Nijeriya su haɗa kai wajen kare dimokuraɗiyya da haƙƙoƙin da kundin tsarin mulki ya tanada, tana mai cewa za ta ci gaba da adawa da duk wani yunƙuri na mayar da Nijeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya.














