ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

by Abubakar Sulaiman
3 hours ago
Inec

Jam’iyyun siyasa sun yi maraba da hukuncin babban kotun tarayya wanda ta soke wasu sassa na jadawalin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) na zaɓen 2027, sun bayyana hukuncin a matsayin babban sauƙi bayan watanni da suka safe suna ƙorafe-ƙorafe kan lokutan hukumar zaɓe.

Hukuncin na iya sauya yadda ake lissafin siyasa kafin zaɓen 2027, bayan ƙorafe-ƙorafen jam’iyyun siyasa kan cewa jadawalin INEC ya yi kaɗan wajen samun damar gudanar da shirye-shirye na ayyukansu yadda ya kamata.

“Akwai buƙatar a yi a hankali kan muhimman tsarin dimokuraɗiyya. Ina da tabbacin cewa dukkan jam’iyyun siyasa sun yi farin ciki da hukuncin. Hukuncin zai taimaka wa jam’iyyun wajen ƙara tsara kansu yadda ya kamata,” mai magana da yawun kwamitin gudanarwa na ƙasa na PDP ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki da Ini Ememobong.

ADVERTISEMENT

Yayin da yake magana kan lamarin, sakataren yaɗa labarai na kwamitin gudanarwa na PDP ɓangaren tsakin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike da Mohammed Haruna Jungudo, ya ce a ɓangarensu har yanzu suna sake yin Nazari dangane da hukuncin kotun.

Ya ce, “Zan sake dawowa gare ku. Muna nazarin hukuncin a halin yanzu,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

Kazalika, sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar PRP, Muhammed Bello Ishaƙ, ya ce hukuncin ya bayyana ƙarfin ikon da jam’iyyun siyasa suke da shi da INEC ta karɓe daga garesu.

Ya ce, “A bayyana yake cewa, hukuncin ya sake ingantawa da ci gaban dimokuraɗiyyarmu ta hanyar mayar da ƙarfin ikon jam’iyyun siyasa wanda INEC ta karɓa da kanta.

“Ya faɗaɗa damar yanke shawara a cikin jam’iyyun siyasa kuma ya cire tsarin da ba shi da kyau a cikin ayyukanmu.”

“INEC na iya ɗaukaka ƙara, ko da yake muna fatan cewa manyan masu ruwa da tsaki za su shiga tsakani don dakatar da irin wannan mataki,” in ji shi.

Ishaƙ ya kuma iƙirarin cewa jam’iyyar APC na iya zama ɗaya daga cikin manyan masu amfani da hukuncin duba da rikice-rikicen cikin gida da take fama da shi wajen fitar da ƴan takara.

Ya ce, “Jam’iyyar mai mulki ta APC na iya zama babbar wacce ta fi amfana daga wannan hukunci, bisa la’akari da halin da take ciki a halin yanzu, wajen magance damuwar da ke ƙara tasowa daga ƙoƙarinta na zaɓan ƴan takaranta.

“Wasu jam’iyyun siyasa ma za su kasance cikin tunanin yadda wannan hukunci zai iya taimaka musu wajen faɗaɗa mambobinsu da inganta shugabanninsu,” in ji shi.

Inec
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
  • Abubakar Sulaiman
    TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
  • Abubakar Sulaiman
    Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

MASU ALAKA

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed
Siyasa

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Siyasa

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Next Post
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.