Jam’iyyun siyasa sun yi maraba da hukuncin babban kotun tarayya wanda ta soke wasu sassa na jadawalin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) na zaɓen 2027, sun bayyana hukuncin a matsayin babban sauƙi bayan watanni da suka safe suna ƙorafe-ƙorafe kan lokutan hukumar zaɓe.
Hukuncin na iya sauya yadda ake lissafin siyasa kafin zaɓen 2027, bayan ƙorafe-ƙorafen jam’iyyun siyasa kan cewa jadawalin INEC ya yi kaɗan wajen samun damar gudanar da shirye-shirye na ayyukansu yadda ya kamata.
“Akwai buƙatar a yi a hankali kan muhimman tsarin dimokuraɗiyya. Ina da tabbacin cewa dukkan jam’iyyun siyasa sun yi farin ciki da hukuncin. Hukuncin zai taimaka wa jam’iyyun wajen ƙara tsara kansu yadda ya kamata,” mai magana da yawun kwamitin gudanarwa na ƙasa na PDP ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki da Ini Ememobong.
Yayin da yake magana kan lamarin, sakataren yaɗa labarai na kwamitin gudanarwa na PDP ɓangaren tsakin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike da Mohammed Haruna Jungudo, ya ce a ɓangarensu har yanzu suna sake yin Nazari dangane da hukuncin kotun.
Ya ce, “Zan sake dawowa gare ku. Muna nazarin hukuncin a halin yanzu,” in ji shi.
Kazalika, sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar PRP, Muhammed Bello Ishaƙ, ya ce hukuncin ya bayyana ƙarfin ikon da jam’iyyun siyasa suke da shi da INEC ta karɓe daga garesu.
Ya ce, “A bayyana yake cewa, hukuncin ya sake ingantawa da ci gaban dimokuraɗiyyarmu ta hanyar mayar da ƙarfin ikon jam’iyyun siyasa wanda INEC ta karɓa da kanta.
“Ya faɗaɗa damar yanke shawara a cikin jam’iyyun siyasa kuma ya cire tsarin da ba shi da kyau a cikin ayyukanmu.”
“INEC na iya ɗaukaka ƙara, ko da yake muna fatan cewa manyan masu ruwa da tsaki za su shiga tsakani don dakatar da irin wannan mataki,” in ji shi.
Ishaƙ ya kuma iƙirarin cewa jam’iyyar APC na iya zama ɗaya daga cikin manyan masu amfani da hukuncin duba da rikice-rikicen cikin gida da take fama da shi wajen fitar da ƴan takara.
Ya ce, “Jam’iyyar mai mulki ta APC na iya zama babbar wacce ta fi amfana daga wannan hukunci, bisa la’akari da halin da take ciki a halin yanzu, wajen magance damuwar da ke ƙara tasowa daga ƙoƙarinta na zaɓan ƴan takaranta.
“Wasu jam’iyyun siyasa ma za su kasance cikin tunanin yadda wannan hukunci zai iya taimaka musu wajen faɗaɗa mambobinsu da inganta shugabanninsu,” in ji shi.














