ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
Inec

Jam’iyyun siyasa sun yi maraba da hukuncin babban kotun tarayya wanda ta soke wasu sassa na jadawalin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) na zaɓen 2027, sun bayyana hukuncin a matsayin babban sauƙi bayan watanni da suka safe suna ƙorafe-ƙorafe kan lokutan hukumar zaɓe.

Hukuncin na iya sauya yadda ake lissafin siyasa kafin zaɓen 2027, bayan ƙorafe-ƙorafen jam’iyyun siyasa kan cewa jadawalin INEC ya yi kaɗan wajen samun damar gudanar da shirye-shirye na ayyukansu yadda ya kamata.

“Akwai buƙatar a yi a hankali kan muhimman tsarin dimokuraɗiyya. Ina da tabbacin cewa dukkan jam’iyyun siyasa sun yi farin ciki da hukuncin. Hukuncin zai taimaka wa jam’iyyun wajen ƙara tsara kansu yadda ya kamata,” mai magana da yawun kwamitin gudanarwa na ƙasa na PDP ƙarƙashin jagorancin Kabiru Turaki da Ini Ememobong.

ADVERTISEMENT

Yayin da yake magana kan lamarin, sakataren yaɗa labarai na kwamitin gudanarwa na PDP ɓangaren tsakin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike da Mohammed Haruna Jungudo, ya ce a ɓangarensu har yanzu suna sake yin Nazari dangane da hukuncin kotun.

Ya ce, “Zan sake dawowa gare ku. Muna nazarin hukuncin a halin yanzu,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Kazalika, sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyyar PRP, Muhammed Bello Ishaƙ, ya ce hukuncin ya bayyana ƙarfin ikon da jam’iyyun siyasa suke da shi da INEC ta karɓe daga garesu.

Ya ce, “A bayyana yake cewa, hukuncin ya sake ingantawa da ci gaban dimokuraɗiyyarmu ta hanyar mayar da ƙarfin ikon jam’iyyun siyasa wanda INEC ta karɓa da kanta.

“Ya faɗaɗa damar yanke shawara a cikin jam’iyyun siyasa kuma ya cire tsarin da ba shi da kyau a cikin ayyukanmu.”

“INEC na iya ɗaukaka ƙara, ko da yake muna fatan cewa manyan masu ruwa da tsaki za su shiga tsakani don dakatar da irin wannan mataki,” in ji shi.

Ishaƙ ya kuma iƙirarin cewa jam’iyyar APC na iya zama ɗaya daga cikin manyan masu amfani da hukuncin duba da rikice-rikicen cikin gida da take fama da shi wajen fitar da ƴan takara.

Ya ce, “Jam’iyyar mai mulki ta APC na iya zama babbar wacce ta fi amfana daga wannan hukunci, bisa la’akari da halin da take ciki a halin yanzu, wajen magance damuwar da ke ƙara tasowa daga ƙoƙarinta na zaɓan ƴan takaranta.

“Wasu jam’iyyun siyasa ma za su kasance cikin tunanin yadda wannan hukunci zai iya taimaka musu wajen faɗaɗa mambobinsu da inganta shugabanninsu,” in ji shi.

Inec
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.