ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Duk Da Matsalolin Tattalin Arziki, Bangaren Inshora Da Hannun Jari Sun Bunkasa

by Bello Hamza
2 years ago
Arziki

Bayani ya nuna cewa, shekarar 2023 ta zo da armashi ga banaren harkokin inshora da masu zuba hannun jari a inda masu zuba jari suka samu ribar fiye da Naira Tiriliyan 11.7 yayin da masu harkar inshora suka tashi da ribar fiye da na naira tiriliyan 1, kamar yadda jaridar LEADERSHIP Sunday ta nakalto mana.

Wannan yana faruwa ne duk da tsananin matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta wanda ya yi sanadiyyar mutuwa manya da kananan kamfanoni da dama ya kuma yi sanadiyyar ficewa wasu manyan kamfanoni daga Nijeriya.

Kasuwar hannun jari ta samu ribar naira tiriliyan 11.734 a daidai ranar 14 ga watan Disamba na wannan shekarar 2023, ana kuma da fatan dorewar wannan nasarar har zuwa karshen shekara da farkon shekara mai kamawa.

ADVERTISEMENT

Tun da farkon wannan shekarar an lura da bunksar kasuwar hannun jari inda masu sayen hannayen jari suka karu suna kuma sayen hanun jari masu yawan gaske.

Ribar hannun jarin da aka samu ya tashi daga Naira tiriliyan 11.734 zuwa naira tiriliyan 27.915 a farkon shekarar 2023 zuwa Naira Tiriliyan 39.649 a daidai ranar 14 ga watan Disamba na shekarar 2023.

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Haka kuma kudin hadahadar musaya a Nijeriya ya tashi da kashi 41.37 daga maki 51,251.06 a ranar 30 ga watan Disamba 2022 zuwa maki 72,455.83 a daidai ranar 14 ga watan Disamba 2023.

Shugaban kamfanin harkar hannun jari mai suna Mike Ezeh, ya bayyana cewa, bayyanar Shugaba Tinubu a mastayin shugaban kasa ya taimaka wajen farfado da kasuwar hannun jari a Nijeriya, musamman yadda zaben 2023 ya zo ba tare da wasu rikice-rikice ba, wadannan ne suka bai wa masu zuba jari kwarin gwiwa da sake jiki wajen sayen hannun jari a Nijeriya.

Haka kuma bangaren inshora ya samu ribar Naira biliyan 729.1 a zango na uku na wannan shekarar an kuma yi hasashen zai iya kaiwa tiriliyan 1 a zango na farfro na shekara mai kamawa, in har haka ya faru kuwu zai kasance kenan a karon farko da ake samu irin wannan ci gaban a cikin shekara 8.

‘Yan Nijeriya sun ci gaba da yankar inshorar rayuwa (Life Insuarance) musamman ganin matsalolin rashin tsaro don iyalansu su samu abin rufa wa kansu asiri in sun mutu, an tabbatar da cewa, iyalai sun kashe naira biliyan 265.39 a yankar inshorar rayuwa a cikin wata 9 duk kuwa da matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta.

Arziki
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
Dalilinmu Na Karkata Ga Cin Bashin Cibiyoyin Kudi Na Musulunci – Ministan Kudi

Dalilinmu Na Karkata Ga Cin Bashin Cibiyoyin Kudi Na Musulunci – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.