ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Duk Da Matsalolin Tattalin Arziki, Bangaren Inshora Da Hannun Jari Sun Bunkasa

by Bello Hamza
3 years ago
Arziki

Bayani ya nuna cewa, shekarar 2023 ta zo da armashi ga banaren harkokin inshora da masu zuba hannun jari a inda masu zuba jari suka samu ribar fiye da Naira Tiriliyan 11.7 yayin da masu harkar inshora suka tashi da ribar fiye da na naira tiriliyan 1, kamar yadda jaridar LEADERSHIP Sunday ta nakalto mana.

Wannan yana faruwa ne duk da tsananin matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta wanda ya yi sanadiyyar mutuwa manya da kananan kamfanoni da dama ya kuma yi sanadiyyar ficewa wasu manyan kamfanoni daga Nijeriya.

Kasuwar hannun jari ta samu ribar naira tiriliyan 11.734 a daidai ranar 14 ga watan Disamba na wannan shekarar 2023, ana kuma da fatan dorewar wannan nasarar har zuwa karshen shekara da farkon shekara mai kamawa.

ADVERTISEMENT

Tun da farkon wannan shekarar an lura da bunksar kasuwar hannun jari inda masu sayen hannayen jari suka karu suna kuma sayen hanun jari masu yawan gaske.

Ribar hannun jarin da aka samu ya tashi daga Naira tiriliyan 11.734 zuwa naira tiriliyan 27.915 a farkon shekarar 2023 zuwa Naira Tiriliyan 39.649 a daidai ranar 14 ga watan Disamba na shekarar 2023.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Haka kuma kudin hadahadar musaya a Nijeriya ya tashi da kashi 41.37 daga maki 51,251.06 a ranar 30 ga watan Disamba 2022 zuwa maki 72,455.83 a daidai ranar 14 ga watan Disamba 2023.

Shugaban kamfanin harkar hannun jari mai suna Mike Ezeh, ya bayyana cewa, bayyanar Shugaba Tinubu a mastayin shugaban kasa ya taimaka wajen farfado da kasuwar hannun jari a Nijeriya, musamman yadda zaben 2023 ya zo ba tare da wasu rikice-rikice ba, wadannan ne suka bai wa masu zuba jari kwarin gwiwa da sake jiki wajen sayen hannun jari a Nijeriya.

Haka kuma bangaren inshora ya samu ribar Naira biliyan 729.1 a zango na uku na wannan shekarar an kuma yi hasashen zai iya kaiwa tiriliyan 1 a zango na farfro na shekara mai kamawa, in har haka ya faru kuwu zai kasance kenan a karon farko da ake samu irin wannan ci gaban a cikin shekara 8.

‘Yan Nijeriya sun ci gaba da yankar inshorar rayuwa (Life Insuarance) musamman ganin matsalolin rashin tsaro don iyalansu su samu abin rufa wa kansu asiri in sun mutu, an tabbatar da cewa, iyalai sun kashe naira biliyan 265.39 a yankar inshorar rayuwa a cikin wata 9 duk kuwa da matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta.

Arziki
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Dalilinmu Na Karkata Ga Cin Bashin Cibiyoyin Kudi Na Musulunci – Ministan Kudi

Dalilinmu Na Karkata Ga Cin Bashin Cibiyoyin Kudi Na Musulunci – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.