ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Duk Da Matsalolin Tattalin Arziki, Bangaren Inshora Da Hannun Jari Sun Bunkasa

by Bello Hamza
3 years ago
Arziki

Bayani ya nuna cewa, shekarar 2023 ta zo da armashi ga banaren harkokin inshora da masu zuba hannun jari a inda masu zuba jari suka samu ribar fiye da Naira Tiriliyan 11.7 yayin da masu harkar inshora suka tashi da ribar fiye da na naira tiriliyan 1, kamar yadda jaridar LEADERSHIP Sunday ta nakalto mana.

Wannan yana faruwa ne duk da tsananin matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta wanda ya yi sanadiyyar mutuwa manya da kananan kamfanoni da dama ya kuma yi sanadiyyar ficewa wasu manyan kamfanoni daga Nijeriya.

Kasuwar hannun jari ta samu ribar naira tiriliyan 11.734 a daidai ranar 14 ga watan Disamba na wannan shekarar 2023, ana kuma da fatan dorewar wannan nasarar har zuwa karshen shekara da farkon shekara mai kamawa.

ADVERTISEMENT

Tun da farkon wannan shekarar an lura da bunksar kasuwar hannun jari inda masu sayen hannayen jari suka karu suna kuma sayen hanun jari masu yawan gaske.

Ribar hannun jarin da aka samu ya tashi daga Naira tiriliyan 11.734 zuwa naira tiriliyan 27.915 a farkon shekarar 2023 zuwa Naira Tiriliyan 39.649 a daidai ranar 14 ga watan Disamba na shekarar 2023.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Haka kuma kudin hadahadar musaya a Nijeriya ya tashi da kashi 41.37 daga maki 51,251.06 a ranar 30 ga watan Disamba 2022 zuwa maki 72,455.83 a daidai ranar 14 ga watan Disamba 2023.

Shugaban kamfanin harkar hannun jari mai suna Mike Ezeh, ya bayyana cewa, bayyanar Shugaba Tinubu a mastayin shugaban kasa ya taimaka wajen farfado da kasuwar hannun jari a Nijeriya, musamman yadda zaben 2023 ya zo ba tare da wasu rikice-rikice ba, wadannan ne suka bai wa masu zuba jari kwarin gwiwa da sake jiki wajen sayen hannun jari a Nijeriya.

Haka kuma bangaren inshora ya samu ribar Naira biliyan 729.1 a zango na uku na wannan shekarar an kuma yi hasashen zai iya kaiwa tiriliyan 1 a zango na farfro na shekara mai kamawa, in har haka ya faru kuwu zai kasance kenan a karon farko da ake samu irin wannan ci gaban a cikin shekara 8.

‘Yan Nijeriya sun ci gaba da yankar inshorar rayuwa (Life Insuarance) musamman ganin matsalolin rashin tsaro don iyalansu su samu abin rufa wa kansu asiri in sun mutu, an tabbatar da cewa, iyalai sun kashe naira biliyan 265.39 a yankar inshorar rayuwa a cikin wata 9 duk kuwa da matsalolin tattalin arzikin da ake fuskanta.

Arziki
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Dalilinmu Na Karkata Ga Cin Bashin Cibiyoyin Kudi Na Musulunci – Ministan Kudi

Dalilinmu Na Karkata Ga Cin Bashin Cibiyoyin Kudi Na Musulunci – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.