ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

by Bello Hamza
7 hours ago
Uwargidan

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka a Hadejia ta Jihar Jigawa, waɗanda suka da haɗa Cibiyar Fasaha ta Bola Ahmed Tinubu da Asibitin Wankin Ƙoda, Tituna da kuma Rumbum Tanada Abinci, domin bunƙasa ilimin fasahar zamani, ƙarfafa ayyukan kiwon lafiya, inganta hanyoyi da kuma tabbatar da wadatar abinci,daidai da manufar Shugaban Ƙasa ta Renewed Hope Agenda.

Cibiyar Fasaha ta Bola Ahmed Tinubu, wadda Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA) ta samar, za ta kasance cikakkiyar cibiyar ƙirƙire-ƙirƙire da fasahar zamani. Cibiyar ta ƙunshi ɗakin bincike na zamani (FabLab) don nazarin basirar AI, na’urorin mutum-mutumi (Robotics) da fasahar kiwon lafiya, tare da cibiyar ƙirƙire-ƙirƙire mai amfani da AI da kuma haɓaka kamfanoni masu tasowa (Startup Incubation Centre). Har ila yau, an tanadi ɗakunan jarabawar kwamfuta (CBT), wuraren aiki na haɗin gwiwa, babban zauren taro na zamani da kuma masaukin ɗalibai mai ɗaukar mutane 60.

Uwargidan Shugaban Ƙasar ta kuma ƙaddamar da Asibitin Sanata Oluremi Tinubu da Cibiyar Wankin Koda, wanda aka gina domin girmama ta, kuma gidauniyar FutureMap Foundation tare da eHealth Africa suka gina tare da cikakken kayan aikin likitanci na zamani, ciki har da na’urorin gwaje-gwaje da wankin ƙoda, domin faɗaɗa samun ingantaccen kiwon lafiya ga al’ummomin da ba su samun da isasshiyar kulawa.

ADVERTISEMENT

Domin tabbatar da ci gaba da samar da ingantattun ayyukan lafiya, asibitin ya haɗa da ɗakunan gwaje-gwaje na zamani, cibiyar wankin ƙoda, dakin tiyata da kuma sashen kula da mata masu juna biyu da haihuwa. Haka kuma, an tanadi tsarin samar da iskar shaka (oɗygen) na zamani, yayin da cibiyar ke amfani da makamashi mai sabuntawa domin tabbatar da cewa babu katsewar ayyukan lafiya.

Da take jawabi yayin ƙaddamarwar, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta buƙaci matasa da su yi amfani da damar da cibiyar ke bayarwa domin ba da gudummawa wajen sauya fasalin tattalin arzikin Najeriya ta hanyar fasahar zamani. Ta kuma yaba wa Darakta Janar na NITDA, Kashifu Inuwa Abdullahi, CCIE, bisa jajircewarsa wajen tabbatar da cewa al’ummomi a faɗin asar nan suna cin moriyar fasaha da ƙirƙire-ƙirƙire.

LABARAI MASU NASABA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Ƙaddamarwar ta kasance wani ɓangare na ziyarar farko da Uwargidan Shugaban Ƙasar ta kai Jihar Jigawa, inda ta kuma ƙaddamar da Shirin Rumbum Abinci na Ƙasa na Yankin Arewa maso Yamma, tare da buɗe wasu muhimman ayyukan more rayuwa, ciki har da Titin Bola Ahmed da Titin Oluremi Tinubu, wanda hakan ke ƙara nuna jajircewar gwamnatin Renewed Hope wajen faɗaɗa damar samun fasahar zamani, ingantaccen kiwon lafiya da ci gaban ƙasa mai haɗa kowa da kowa.

Uwargidan
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

MASU ALAKA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Next Post
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

LABARAI MASU NASABA

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.