ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

by Bello Hamza
2 months ago
Uwargidan

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka a Hadejia ta Jihar Jigawa, waɗanda suka da haɗa Cibiyar Fasaha ta Bola Ahmed Tinubu da Asibitin Wankin Ƙoda, Tituna da kuma Rumbum Tanada Abinci, domin bunƙasa ilimin fasahar zamani, ƙarfafa ayyukan kiwon lafiya, inganta hanyoyi da kuma tabbatar da wadatar abinci,daidai da manufar Shugaban Ƙasa ta Renewed Hope Agenda.

Cibiyar Fasaha ta Bola Ahmed Tinubu, wadda Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA) ta samar, za ta kasance cikakkiyar cibiyar ƙirƙire-ƙirƙire da fasahar zamani. Cibiyar ta ƙunshi ɗakin bincike na zamani (FabLab) don nazarin basirar AI, na’urorin mutum-mutumi (Robotics) da fasahar kiwon lafiya, tare da cibiyar ƙirƙire-ƙirƙire mai amfani da AI da kuma haɓaka kamfanoni masu tasowa (Startup Incubation Centre). Har ila yau, an tanadi ɗakunan jarabawar kwamfuta (CBT), wuraren aiki na haɗin gwiwa, babban zauren taro na zamani da kuma masaukin ɗalibai mai ɗaukar mutane 60.

Uwargidan Shugaban Ƙasar ta kuma ƙaddamar da Asibitin Sanata Oluremi Tinubu da Cibiyar Wankin Koda, wanda aka gina domin girmama ta, kuma gidauniyar FutureMap Foundation tare da eHealth Africa suka gina tare da cikakken kayan aikin likitanci na zamani, ciki har da na’urorin gwaje-gwaje da wankin ƙoda, domin faɗaɗa samun ingantaccen kiwon lafiya ga al’ummomin da ba su samun da isasshiyar kulawa.

ADVERTISEMENT

Domin tabbatar da ci gaba da samar da ingantattun ayyukan lafiya, asibitin ya haɗa da ɗakunan gwaje-gwaje na zamani, cibiyar wankin ƙoda, dakin tiyata da kuma sashen kula da mata masu juna biyu da haihuwa. Haka kuma, an tanadi tsarin samar da iskar shaka (oɗygen) na zamani, yayin da cibiyar ke amfani da makamashi mai sabuntawa domin tabbatar da cewa babu katsewar ayyukan lafiya.

Da take jawabi yayin ƙaddamarwar, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta buƙaci matasa da su yi amfani da damar da cibiyar ke bayarwa domin ba da gudummawa wajen sauya fasalin tattalin arzikin Najeriya ta hanyar fasahar zamani. Ta kuma yaba wa Darakta Janar na NITDA, Kashifu Inuwa Abdullahi, CCIE, bisa jajircewarsa wajen tabbatar da cewa al’ummomi a faɗin asar nan suna cin moriyar fasaha da ƙirƙire-ƙirƙire.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ƙaddamarwar ta kasance wani ɓangare na ziyarar farko da Uwargidan Shugaban Ƙasar ta kai Jihar Jigawa, inda ta kuma ƙaddamar da Shirin Rumbum Abinci na Ƙasa na Yankin Arewa maso Yamma, tare da buɗe wasu muhimman ayyukan more rayuwa, ciki har da Titin Bola Ahmed da Titin Oluremi Tinubu, wanda hakan ke ƙara nuna jajircewar gwamnatin Renewed Hope wajen faɗaɗa damar samun fasahar zamani, ingantaccen kiwon lafiya da ci gaban ƙasa mai haɗa kowa da kowa.

Uwargidan
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.