ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Jam’iyyu 18 Ne Za Su Yi Takarar Gwamna A Jihohi 28, ‘Yan Takara 10,231 Ke Neman Kujerar Majalisar Dokoki —INEC

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta fitar da sunaye 837 na ‘yan takarar gwamna da na mataimakan su, waɗanda za su fafata a zaɓen 2023.

Kakakin Yaɗa Labaran INEC Festus Okoye ne ya bayyana sanarwar fitar da sunayen a shafin yanar gizo na INEC, a ranar Laraba.

  • Kada Wata Jam’iyya Ta Kuskura Ta Karɓi Tallafin Kuɗi Daga Ƙasashen Waje – INEC

Sunayen dai su na da yawan da ya kai shafuka 894, waɗanda su ka haɗa na ‘yan takarar gwamnoni da mataimakan su 837, sai kuma na masu takarar majalisar dokoki har mutum 10,231.

ADVERTISEMENT

Okoye ya ce za a yi zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin a jihohi 28.

Ya ƙara da cewa tun a ranar 12 ga Agusta, 2022 INEC da kulle damar canja ɗan takara ko janyewa, sai fa idan lamari ne na mutuwa ya ratsa.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

“Kai ko da ɗan takara ne ya mutu, to tilas sai dai kotu ce za ta bai wa INEC iznin amincewa ta amshi sunan wanda zai maye gurbin sa, kamar yadda Dokar Zaɓe ta Sashe na 34 (1) ta 2022 ta gindiya.”

Okoye ya ce jam’iyyu 18 ne su za su yi takarar zaɓen gwamna da na Majalisar Dokoki.

Cikin makon shekaranjiya ne wannan jarida ta buga labarin cewa za a fafata da mata 380 cikin ‘yan takarar kujerun Majalisar Dattawa da ta Tarayya su 4,224.

A jadawalin sunayen ‘yan takarar da ta fitar, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa an samu mace ɗaya tilo ta fito takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

Hakan na ƙunshe cikin jerin sunayen da hukumar ta fitar, mai ɗauke sa hannun Kakakin Yaɗa Labarai na INEC, Festus Okoye.

Ya ce an samu mata har 380 da za a fafata neman kujerun Majalisar Tarayya da Majalisar Dattawa da su.

A jerin sunayen an lissafa mata 92 masu neman kujerar Majalisar Dattawa, sai kuma wasu mata 288 da za a fafata neman kujerar Majalisar Tarayya da su.

A ɓangaren maza kuwa, INEC ta buga sunayen 1,008 masu neman kujerar Majalisar Dattawa, sai kuma wasu 2,832 da za su fafata neman kujerun Majalisar Tarayya.

INEC ta ce jam’iyyu 18 ne su ka shiga takarar zaɓen shugaban ƙasa, wanda za a fafata a ranar 25 ga Fabrairu, 2023.

“An samu masu takarar shugaban ƙasa da masu takarar mataimakin shugaban ƙasa har su 35 daga jam’iyyu 18. Akwai ‘yan takarar Majalisar Dattawa su 1,101, waɗanda a cikin su 92 mata ne. Sai kuma masu takarar Majalisar Tarayya su 3122.

“Za a yi takarar kujeru 109 a Majalisar Dattawa, sai kuma kujeru 360 a Majalisar Tarayya. Baki ɗaya kujeru 469 kenan.” Inji Okoye, wanda ya ƙara da cewa waɗannan ‘yan takara na majalisu sun zama 4,224 kenan.

Cikin waɗanda INEC ta wanke domin shiga takarar zaɓen Shugaban Ƙasa, har da Bola Tinubu na APC, Rabiu Kwankwaso na NNPP, Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP.

Sai dai kuma duk da jam’iyyar ADC ta dakatar da Kachikwu ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar, sunan sa ya fito a cikin waɗanda za su fafata.

A jerin sunayen masu takarar Majalisar Dattawa dai babu sunan Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan na APC da Machina wanda su ke tankiyar cancantar shiga takarar a tsakanin su.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar 10 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Hutu 

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar 10 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Hutu 

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.