ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Jam’iyyu 18 Ne Za Su Yi Takarar Gwamna A Jihohi 28, ‘Yan Takara 10,231 Ke Neman Kujerar Majalisar Dokoki —INEC

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta fitar da sunaye 837 na ‘yan takarar gwamna da na mataimakan su, waɗanda za su fafata a zaɓen 2023.

Kakakin Yaɗa Labaran INEC Festus Okoye ne ya bayyana sanarwar fitar da sunayen a shafin yanar gizo na INEC, a ranar Laraba.

  • Kada Wata Jam’iyya Ta Kuskura Ta Karɓi Tallafin Kuɗi Daga Ƙasashen Waje – INEC

Sunayen dai su na da yawan da ya kai shafuka 894, waɗanda su ka haɗa na ‘yan takarar gwamnoni da mataimakan su 837, sai kuma na masu takarar majalisar dokoki har mutum 10,231.

ADVERTISEMENT

Okoye ya ce za a yi zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin a jihohi 28.

Ya ƙara da cewa tun a ranar 12 ga Agusta, 2022 INEC da kulle damar canja ɗan takara ko janyewa, sai fa idan lamari ne na mutuwa ya ratsa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

“Kai ko da ɗan takara ne ya mutu, to tilas sai dai kotu ce za ta bai wa INEC iznin amincewa ta amshi sunan wanda zai maye gurbin sa, kamar yadda Dokar Zaɓe ta Sashe na 34 (1) ta 2022 ta gindiya.”

Okoye ya ce jam’iyyu 18 ne su za su yi takarar zaɓen gwamna da na Majalisar Dokoki.

Cikin makon shekaranjiya ne wannan jarida ta buga labarin cewa za a fafata da mata 380 cikin ‘yan takarar kujerun Majalisar Dattawa da ta Tarayya su 4,224.

A jadawalin sunayen ‘yan takarar da ta fitar, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa an samu mace ɗaya tilo ta fito takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

Hakan na ƙunshe cikin jerin sunayen da hukumar ta fitar, mai ɗauke sa hannun Kakakin Yaɗa Labarai na INEC, Festus Okoye.

Ya ce an samu mata har 380 da za a fafata neman kujerun Majalisar Tarayya da Majalisar Dattawa da su.

A jerin sunayen an lissafa mata 92 masu neman kujerar Majalisar Dattawa, sai kuma wasu mata 288 da za a fafata neman kujerar Majalisar Tarayya da su.

A ɓangaren maza kuwa, INEC ta buga sunayen 1,008 masu neman kujerar Majalisar Dattawa, sai kuma wasu 2,832 da za su fafata neman kujerun Majalisar Tarayya.

INEC ta ce jam’iyyu 18 ne su ka shiga takarar zaɓen shugaban ƙasa, wanda za a fafata a ranar 25 ga Fabrairu, 2023.

“An samu masu takarar shugaban ƙasa da masu takarar mataimakin shugaban ƙasa har su 35 daga jam’iyyu 18. Akwai ‘yan takarar Majalisar Dattawa su 1,101, waɗanda a cikin su 92 mata ne. Sai kuma masu takarar Majalisar Tarayya su 3122.

“Za a yi takarar kujeru 109 a Majalisar Dattawa, sai kuma kujeru 360 a Majalisar Tarayya. Baki ɗaya kujeru 469 kenan.” Inji Okoye, wanda ya ƙara da cewa waɗannan ‘yan takara na majalisu sun zama 4,224 kenan.

Cikin waɗanda INEC ta wanke domin shiga takarar zaɓen Shugaban Ƙasa, har da Bola Tinubu na APC, Rabiu Kwankwaso na NNPP, Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP.

Sai dai kuma duk da jam’iyyar ADC ta dakatar da Kachikwu ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar, sunan sa ya fito a cikin waɗanda za su fafata.

A jerin sunayen masu takarar Majalisar Dattawa dai babu sunan Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan na APC da Machina wanda su ke tankiyar cancantar shiga takarar a tsakanin su.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
  • Sulaiman
    Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar 10 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Hutu 

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar 10 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Hutu 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.