Jam’iyyar adawa ta ADC ta tabbatar da samun lambar shiga manhajar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) domin ɗora sunayen ’yan takararta da za su shiga zaɓen shekarar 2027.
An tabbatar da hakan ne ga Daily Trust daga bakin Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi.
Mai magana da yawun jam’iyyar ya ce:”Mun karɓi lambobin shiga manhajar INEC domin ɗora sunayen ‘yan takara tun a makon da ya gabata.”
Jam’iyyar ADC ta tsinci kanta cikin rikicin shugabanci tun bayan bayyanar Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC) na yanzu ƙarƙashin jagorancin David Mark.
A ranar Litinin kuma, wani tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC ya yi zargin cewa akwai wani sabon yunkuri da wasu mutane ke yi domin hana jam’iyyar ADC shiga zaɓukan da ke tafe.
Amma har yanzu, ADC da INEC ba su fitar da ƙarin bayani kan wannan batu ba a lokacin haɗa wannan rahoto.














