A bana ake cika shekaru 105 da kafa Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin (JKS). Karkashin jagorancin jam’iyyar, Sinawa sun cimma manyan nasarorin da suka ja hankalin duniya.Mene ne dalilin da ya sa JKS ke iya cika alkawuran da ta dauka a ko da yaushe? Domin gano amsar, kafar CGTN ta gudanar da wani nazari tsakanin masu bayar da amsa daga kasashe 41, inda mutane 11,521 suka bayyana ra’ayoyinsu.
Yayin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 14 tsakanin shekarar 2021 da 2025, alkaluman tattalin arziki na GDP na kasar Sin sun zarce yuan tiriliyan 140, kimanin dalar Amurka tiriliyan 20, kudin shigar kowane dan kasa kuwa ya karu da kaso 5.4 bisa dari a matsakaicin mataki a shekara, an kirkiro sabbin guraben ayyukan yi miliyan 62.42 a birane, kana tsawon rayuwar jama’a ya karu zuwa sama da shekaru 79. Cikin nazarin, kaso 63.9 bisa dari na masu bayar da amsa sun amince cewa ba za a iya raba nasarorin da zamanantarwar irin ta kasar Sin ta samu da nagartattun dabarun JKS ba. Wannan ra’ayi ya fi karfi a gurin masu bayar da amsa daga kasashe masu tasowa, inda kaso 71.4 bisa dari suka amince da shi.
Daga cikin tarin dabarun shugabanci na JKS, masu bayar da amsa sun zabi wasu abubuwa hudu da suka cancanci a yi koyi da su, wadanda suka hada da “bayar da fifiko ga rayuwar jama’a da kuma kyautata ta,” da “tsarawa da aiwatar da shirye-shiryen raya kasa masu dogon zango,” da “daukar ingantattun matakan yaki da cin hanci da rashawa” da kuma “tattara albarkatu yadda ya kamata domin aiwatar da manyan ayyuka.” Idan aka yi la’akari da yankuna, masu bayar da amsa daga nahiyar Afrika sun zabi dabarar “bayar da fifiko ga rayuwar jama’a da kuma kyautata ta” fiye da sauran nahiyoyi, yayin da sama da rabin masu bayar da amsa daga kudancin nahiyar Amurka suka zabi “daukar ingantattun matakan yaki da cin hanci da rashawa” da kuma “tsarawa da aiwatar da shirye-shiryen raya kasa masu dogon zango.” (Fa’iza Mustapha)














